< Ayuba 28 >

1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
“Surely there is a mine for silver, and a place for gold which they refine.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Iron is taken out of the earth, and copper is smelted out of the ore.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Man sets an end to darkness, and searches out, to the furthest bound, the stones of obscurity and of thick darkness.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
He breaks open a shaft away from where people live. They are forgotten by the foot. They hang far from men, they swing back and forth.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
As for the earth, out of it comes bread. Underneath it is turned up as it were by fire.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Sapphires come from its rocks. It has dust of gold.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
That path no bird of prey knows, neither has the falcon’s eye seen it.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
The proud animals have not trodden it, nor has the fierce lion passed by there.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
He puts his hand on the flinty rock, and he overturns the mountains by the roots.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
He cuts out channels among the rocks. His eye sees every precious thing.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
He binds the streams that they don’t trickle. The thing that is hidden he brings out to light.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
“But where will wisdom be found? Where is the place of understanding?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Man doesn’t know its price, and it isn’t found in the land of the living.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
The deep says, ‘It isn’t in me.’ The sea says, ‘It isn’t with me.’
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
It can’t be gotten for gold, neither will silver be weighed for its price.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
It can’t be valued with the gold of Ophir, with the precious onyx, or the sapphire.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Gold and glass can’t equal it, neither will it be exchanged for jewels of fine gold.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
No mention will be made of coral or of crystal. Yes, the price of wisdom is above rubies.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
The topaz of Ethiopia will not equal it. It won’t be valued with pure gold.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Where then does wisdom come from? Where is the place of understanding?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Seeing it is hidden from the eyes of all living, and kept close from the birds of the sky.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Destruction and Death say, ‘We have heard a rumor of it with our ears.’
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
“God understands its way, and he knows its place.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
For he looks to the ends of the earth, and sees under the whole sky.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
He establishes the force of the wind. Yes, he measures out the waters by measure.
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
When he made a decree for the rain, and a way for the lightning of the thunder,
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
then he saw it, and declared it. He established it, yes, and searched it out.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
To man he said, ‘Behold, the fear of the Lord, that is wisdom. To depart from evil is understanding.’”

< Ayuba 28 >