< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job again took up his parable, and said,
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
“Oh that I were as in the months of old, as in the days when God watched over me;
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
when his lamp shone on my head, and by his light I walked through darkness,
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
as I was in my prime, when the friendship of God was in my tent,
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
when the Almighty was yet with me, and my children were around me,
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
when my steps were washed with butter, and the rock poured out streams of oil for me,
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
when I went out to the city gate, when I prepared my seat in the street.
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
The young men saw me and hid themselves. The aged rose up and stood.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
The princes refrained from talking, and laid their hand on their mouth.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
The voice of the nobles was hushed, and their tongue stuck to the roof of their mouth.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
For when the ear heard me, then it blessed me, and when the eye saw me, it commended me,
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
because I delivered the poor who cried, and the fatherless also, who had no one to help him,
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
the blessing of him who was ready to perish came on me, and I caused the widow’s heart to sing for joy.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
I put on righteousness, and it clothed me. My justice was as a robe and a diadem.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
I was eyes to the blind, and feet to the lame.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
I was a father to the needy. I researched the cause of him whom I didn’t know.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
I broke the jaws of the unrighteous and plucked the prey out of his teeth.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Then I said, ‘I will die in my own house, I will count my days as the sand.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
My root is spread out to the waters. The dew lies all night on my branch.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
My glory is fresh in me. My bow is renewed in my hand.’
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
“Men listened to me, waited, and kept silence for my counsel.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
After my words they didn’t speak again. My speech fell on them.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
They waited for me as for the rain. Their mouths drank as with the spring rain.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
I smiled on them when they had no confidence. They didn’t reject the light of my face.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
I chose out their way, and sat as chief. I lived as a king in the army, as one who comforts the mourners.

< Ayuba 29 >