< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Job again took up his parable, and said,
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
“As God lives, who has taken away my right, the Almighty, who has made my soul bitter
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
(for the length of my life is still in me, and the spirit of God is in my nostrils);
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
surely my lips will not speak unrighteousness, neither will my tongue utter deceit.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Far be it from me that I should justify you. Until I die I will not put away my integrity from me.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
I hold fast to my righteousness, and will not let it go. My heart will not reproach me so long as I live.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
“Let my enemy be as the wicked. Let him who rises up against me be as the unrighteous.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
For what is the hope of the godless, when he is cut off, when God takes away his life?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Will God hear his cry when trouble comes on him?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Will he delight himself in the Almighty, and call on God at all times?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
I will teach you about the hand of God. I will not conceal that which is with the Almighty.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Behold, all of you have seen it yourselves; why then have you become altogether vain?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
“This is the portion of a wicked man with God, the heritage of oppressors, which they receive from the Almighty.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
If his children are multiplied, it is for the sword. His offspring will not be satisfied with bread.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Those who remain of him will be buried in death. His widows will make no lamentation.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Though he heap up silver as the dust, and prepare clothing as the clay;
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
he may prepare it, but the just will put it on, and the innocent will divide the silver.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
He builds his house as the moth, as a booth which the watchman makes.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
He lies down rich, but he will not do so again. He opens his eyes, and he is not.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Terrors overtake him like waters. A storm steals him away in the night.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
The east wind carries him away, and he departs. It sweeps him out of his place.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
For it hurls at him, and does not spare, as he flees away from his hand.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Men will clap their hands at him, and will hiss him out of his place.

< Ayuba 27 >