< Ayuba 24 >

1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
“Why aren’t times laid up by the Almighty? Why don’t those who know him see his days?
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
There are people who remove the landmarks. They violently take away flocks, and feed them.
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
They drive away the donkey of the fatherless, and they take the widow’s ox for a pledge.
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
They turn the needy out of the way. The poor of the earth all hide themselves.
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
Behold, as wild donkeys in the desert, they go out to their work, seeking diligently for food. The wilderness yields them bread for their children.
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
They cut their food in the field. They glean the vineyard of the wicked.
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
They lie all night naked without clothing, and have no covering in the cold.
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
They are wet with the showers of the mountains, and embrace the rock for lack of a shelter.
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
There are those who pluck the fatherless from the breast, and take a pledge of the poor,
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
so that they go around naked without clothing. Being hungry, they carry the sheaves.
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
They make oil within the walls of these men. They tread wine presses, and suffer thirst.
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
From out of the populous city, men groan. The soul of the wounded cries out, yet God doesn’t regard the folly.
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
“These are of those who rebel against the light. They don’t know its ways, nor stay in its paths.
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
The murderer rises with the light. He kills the poor and needy. In the night he is like a thief.
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
The eye also of the adulterer waits for the twilight, saying, ‘No eye will see me.’ He disguises his face.
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
In the dark they dig through houses. They shut themselves up in the daytime. They don’t know the light.
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
For the morning is to all of them like thick darkness, for they know the terrors of the thick darkness.
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
“They are foam on the surface of the waters. Their portion is cursed in the earth. They don’t turn into the way of the vineyards.
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
Drought and heat consume the snow waters, so does Sheol those who have sinned. (Sheol h7585)
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
The womb will forget him. The worm will feed sweetly on him. He will be no more remembered. Unrighteousness will be broken as a tree.
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
He devours the barren who don’t bear. He shows no kindness to the widow.
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
Yet God preserves the mighty by his power. He rises up who has no assurance of life.
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
God gives them security, and they rest in it. His eyes are on their ways.
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
They are exalted; yet a little while, and they are gone. Yes, they are brought low, they are taken out of the way as all others, and are cut off as the tops of the ears of grain.
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
If it isn’t so now, who will prove me a liar, and make my speech worth nothing?”

< Ayuba 24 >