< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Then Job answered,
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
“Even today my complaint is rebellious. His hand is heavy in spite of my groaning.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Oh that I knew where I might find him! That I might come even to his seat!
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
I would set my cause in order before him, and fill my mouth with arguments.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
I would know the words which he would answer me, and understand what he would tell me.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Would he contend with me in the greatness of his power? No, but he would listen to me.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
There the upright might reason with him, so I should be delivered forever from my judge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
“If I go east, he is not there. If I go west, I can’t find him.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
He works to the north, but I can’t see him. He turns south, but I can’t catch a glimpse of him.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
But he knows the way that I take. When he has tried me, I will come out like gold.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
My foot has held fast to his steps. I have kept his way, and not turned away.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
I haven’t gone back from the commandment of his lips. I have treasured up the words of his mouth more than my necessary food.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
But he stands alone, and who can oppose him? What his soul desires, even that he does.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
For he performs that which is appointed for me. Many such things are with him.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Therefore I am terrified at his presence. When I consider, I am afraid of him.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
For God has made my heart faint. The Almighty has terrified me.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Because I was not cut off before the darkness, neither did he cover the thick darkness from my face.

< Ayuba 23 >