< Esther 7 >

1 So the king and Haman came in, to banquet with Esther the queen.
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
2 Then said the king unto Esther, on the second day also, during the banquet of wine, What is thy petition, Queen Esther, that it may be granted thee? and what is thy request—unto the half of the kingdom—that it may be performed?
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
3 Then answered Esther the queen, and said, If I have found favour in thine eyes, O king, and if, unto the king, it seem good, let my life be granted me, as my petition, and my people, as my request;
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
4 For we are sold, I and my people, to be destroyed, to be slain and to be caused to perish. If indeed, for bondmen and for bondwomen, we had been sold, I had held my peace, although the adversary could not have made good the damage to the king.
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
5 Then spake King Ahasuerus, and said unto Esther the queen, —Who is he now, and where is he, whose heart is set to act thus?
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
6 And Esther said, A man who is an adversary and enemy, this wicked Haman. And, Haman, was terrified, before the king and the queen.
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
7 Now, the king, arising in his wrath from the banquet of wine, and going into the palace garden, Haman, stood to make request for his life from Esther the queen, for he saw that ruin, was determined against him, by the king.
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
8 When, the king, returned out of the palace garden into the place of the banquet of wine, Haman, was lying prostrate upon the couch whereon Esther was. Then said the king, Will he, even dare to force the queen, while I am in the house? No sooner had the word gone forth out of the mouth of the king, than, the face of Haman, they had covered.
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
9 Then said Harbonah—one of the eunuchs before the king—Yea lo! the gallows that Haman made ready for Mordecai, who had spoken well for the king, is standing in Haman’s house, of a height of fifty cubits. Then said the king, Hang him thereon.
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
10 So they hanged Haman on the gallows which he had prepared for Mordecai, —and, the wrath of the king, was appeased.
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.

< Esther 7 >