< Esther 6 >

1 During that night, the sleep of the king fled, —and he commanded to bring in the book of remembrance, the chronicles, and they were read before the king.
A daren nan, sarki bai iya barci ba, saboda haka ya ba da umarni a kawo, a kuma karanta masa littafin tarihi na shekara-shekara, da rubutaccen labarin mulkinsa.
2 And it was found written, how that Mordecai had told concerning Bigthana and Teresh, the two eunuchs of the king guarding the threshold, —who had sought to thrust forth a hand upon King Ahasuerus.
Aka tarar, a rubuce a ciki, cewa Mordekai ya tone ƙulle-ƙullen Bigtana da Teresh, biyu daga hafsoshin sarki, waɗanda suke tsaron mashigin ƙofa, waɗanda suka ƙulla su kashe Sarki Zerzes.
3 Then said the king, What honour and dignity hath been done unto Mordecai, for this? Then said the king’s young men, who were ministering unto him, Nothing hath been done for him.
Sarki ya ce, “Wace girma da daraja ce aka ba wa Mordekai saboda wannan?” Masu hidimarsa suka ce, “Ba a yi masa wani abu ba.”
4 Then said the king, Who is in the court? Now, Haman, had come into the outer court of the kings house, to speak unto the king, to hang Mordecai, upon the gallows which he had prepared for him.
Sarki ya ce, “Wa yake a haraba?” Daidai lokacin kuwa Haman ya shigo harabar waje na fada don yă yi magana da sarki a kan a rataye Mordekai a wurin rataye mai laifin da ya shirya.
5 So the king’s young men said unto him, Lo! Haman, standing in the court. And the king said, Let him come in.
Masu yi wa sarki hidima, suka amsa, “Haman yana tsaye a haraba.” Sarki ya umarta, “A kawo shi ciki.”
6 So Haman came in, and the king said unto him, What shall be done unto the man in whose honour, the king delighteth? Then said Haman, in his own heart, Unto whom will the king delight to do honour, more than unto me?
Sa’an nan Haman ya shigo, sai sarki ya ce masa, “Me ya kamata a yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama?” Haman dai ya yi tunani a ransa ya ce, “Wane ne sarki zai girmama in ba ni ba?”
7 So Haman said unto the king, —As touching the man in whose honour, the king, delighteth,
Sai ya amsa wa sarki cewa, “Saboda mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama,
8 let them bring in royal apparel wherewith the king hath clothed himself, —and the horse whereon the king hath ridden, and the royal crown which hath been set upon his own head;
bari a kawo rigar sarautar da sarki ya taɓa sawa, da kuma dokin da sarki ya taɓa hawa, wanda aka sa kambin sarauta a kai.
9 and let the apparel and the horse be delivered unto the hand of one of the king’s rulers, one of the nobles, and so let them array the man, in whose honour, the king, delighteth, —and cause him to ride upon the horse through the broadway of the city, and let them proclaim before him, Thus and thus, shall it be done unto the man in whose honour, the king, delighteth!
Sa’an nan, bari a ba da rigar da kuma dokin wa ɗaya daga cikin manyan sarakuna mafi kirki na sarki. Bari shi kuma yă sa wannan riga wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama, a kuma bi da shi a bisan doki ko’ina a titunan birni, ana shela a gabansa ana cewa, ‘Wannan shi ne abin da ake yin wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!’”
10 Then said the king unto Haman, Haste, take the apparel and the horse, just as thou hast said, and do even so unto Mordecai the Jew, who is sitting in the kings gate, —do not let fail a thing, of all which thou hast spoken!
Sarki ya umarci Haman ya ce, “Tafi yanzu ka karɓi rigar da dokin, ka kuma yi yadda ka shawarta wa Mordekai, mutumin Yahudan nan, wanda yake zama a bakin ƙofar sarki. Kada ka kāsa yin kome daga cikin abin da ka faɗa.”
11 So Haman took the apparel and the horse, and arrayed Mordecai, —and caused him to ride through the broadway of the city, and proclaimed before him, Thus and thus, shall it be done unto the man in whoso honour, the king, delighteth!
Saboda haka, Haman ya karɓo rigar da dokin. Ya sa wa Mordekai rigar, ya kuma bi da shi a kan doki ko’ina a titunan birnin, yana shela a gabansa yana cewa, “Wannan shi ne abin da ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!”
12 Then Mordecai returned unto the gate of the king, —but, Haman, hurried unto his own house, mourning, and with covered head.
Daga baya, Mordekai ya dawo zuwa ƙofar sarki. Amma Haman ya ruga gida, kansa a rufe, saboda baƙin ciki.
13 And Haman recounted unto Zeresh his wife, and unto all his friends, everything that had befallen him. Then said his wise men, and Zeresh his wife, unto him, If, of the seed of the Jews, is Mordecai before whom thou hast begun to fall, thou shalt not prevail against him, but shalt, utterly fall, before him.
Ya je ya faɗa wa matarsa Zeresh, da dukan abokansa, me ya same shi. Masu ba shi shawara, da matarsa Zeresh, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara fāɗuwa a gabansa, daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, tabbatacce za ka fāɗi a gabansa!”
14 While yet they were speaking with him, the eunuchs of the king, had come, —and they hastened to bring Haman, unto the banquet which Esther had prepared.
Suna cikin magana da shi ke nan, sai ga bābānnin sarki, suka iso suka kuma hanzarta da Haman zuwa liyafar da Esta ta shirya.

< Esther 6 >