< Esther 8 >

1 On that day, did King Ahasuerus give unto Esther the queen, the house of Haman, the adversary of the Jews, —and, Mordecai, came in before the king, for Esther had told, what he was to her.
A wannan rana, Sarki Zerzes ya ba wa Esta mallakar Haman, abokin gāban Yahudawa. Mordekai kuma ya zo gaban sarki, gama Esta ta faɗa yadda ta haɗa dangi da shi.
2 And the king took off his signet-ring, which he had taken from Haman, and gave it unto Mordecai, —and Esther set Mordecai over the house of Haman.
Sarki ya cire zobensa na hatimi, wanda ya karɓo daga Haman ya ba Mordekai. Esta kuma ta naɗa shi a kan mallakar Haman.
3 Yet again, spake Esther before the king, and fell down at his feet, —and wept and made supplication unto him, to cause the mischief of Haman the Agagite to pass away, even the plot which he had plotted against the Jews.
Esta ta sāke roƙon sarki, ta fāɗi a ƙafafunsa tana kuka. Ta roƙe shi yă kawo ƙarshen mugun shirin nan na Haman, mutumin Agag; wanda ya shirya a kan Yahudawa.
4 And the king held out unto Esther, the golden sceptre, —so Esther arose, and stood before the king;
Sai sarki ya miƙa wa Esta sandan sarauta na zinariya, ta kuwa tashi ta tsaya a gabansa.
5 and said—If, unto the king, it seem good, and if I have found favour before him, and the thing be approved before the king, and, I myself, be pleasing in his eyes, let it be written, to reverse the letters plotted by Haman, son of Hammedatha, the Agagite, which he wrote to destroy thee Jews, who are in all the provinces of the king.
Ta ce, “In sarki ya yarda, in kuma na sami tagomashi daga gare shi, idan kuma ya gamshe shi yă yi abin da yake daidai, idan yana jin daɗina, bari a rubuta umarni a soke hukuncin saƙonin da Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya shirya ya kuma rubuta domin a hallaka Yahudawa a dukan lardunan sarki.
6 For how can I endure to see the ruin that shall overtake my people? or how can I endure to see the destruction of my kindred?
Gama yaya zan jure da ganin masifa ta faɗa a kan mutanena? Yaya zan jure in ga an hallaka iyalina?”
7 Then said King Ahasuerus unto Esther the queen, and unto Mordecai the Jew, —Lo! the house of Haman, have I given unto Esther, and, him, have they hanged upon the gallows, because he thrust forth his hand against the Jews.
Sarki Zerzes ya amsa wa Esta da Mordekai mutumin Yahuda, “Domin Haman ya kai wa Yahudawa hari, na ba da mallakarsa ga Esta, an kuma rataye shi a wurin rataye mai laifi.
8 Ye, therefore, write concerning the Jews as may seem good in your own eyes, in the name of the king, and seal it with the kings signet-ring, —for a writing which hath been written in the king’s name, and sealed with the king’s signet-ring, none can reverse.
Yanzu ku rubuta wata doka, a sunan sarki, a madadin Yahudawa, yadda kuka ga ya fi kyau ku kuma hatimce ta da zoben hatimin sarki, gama babu takardar da aka rubuta da sunan sarki, aka kuma hatimce da zobensa da za a iya sokewa.”
9 Then were called the king’s scribes at that time—in the third month, the same, is the month Siwan, on the twenty-third thereof, and it was written according to all that Mordecai commanded unto the Jews, and unto the satraps and pashas and rulers of the provinces, which are from India even unto Ethiopia, a hundred and twenty-seven provinces, every province according to the writing thereof, and every people according to their tongue, —and unto the Jews, according to their writing, and according to their tongue;
Nan da nan aka kira magatakardun fada, a ranar ashirin da uku ga watan uku, wato, watan Siban. Suka rubuta dukan umarnan Mordekai ga Yahudawa, da kuma ga shugabanni, da gwamnoni, da hakiman larduna 127 tun daga Indiya har zuwa Kush. Aka rubuta waɗannan umarnan a rubutun kowane lardi, da kuma cikin harshen kowane mutane. Aka kuma rubuta ga Yahudawa a rubutunsu da harshensu.
10 and he wrote in the name of King Ahasuerus, and sealed it with the king’s signet-ring, —and sent letters by the hand of runners on horses, riding the swift steeds used in the kings service, bred of the stud:
Mordekai ya yi rubutu da sunan Sarki Zerzes, ya hatimce saƙonin da zoben hatimin sarki, ya kuma aika da su ta hannun masu’yan aika a kan dawakai, waɗanda sukan hau dawakai masu gudu sosai, da aka yi kiwonsu musamman saboda sarki.
11 That the king had granted unto the Jews who were in every city, to gather themselves together, and to stand for their life, to destroy, to slay and to cause to perish—all the force of the people and province who should distress them, their little ones and women, —and [to take] the spoil of them as a prey:
Dokar sarki ta ba wa Yahudawa a kowace birni izini su taru, su kuma kāre kansu, domin su hallaka, su kashe, su kuma hallaka kowace ƙungiyar mayaƙa, na kowace ƙasa, ko lardi, da wataƙila za su kai musu, da matansu, da yaransu hari; su kuma washe mallakar abokan gābansu.
12 upon one day, throughout all the provinces of King Ahasuerus, —upon the thirteenth of the twelfth month, the same, is the month Adar:
Ranar da aka shirya domin Yahudawa su yi wannan a dukan lardunan Sarki Zerzes, ita ce ranar goma sha uku ga watan goma sha biyu, wato, watan Adar.
13 A copy of the writing to be given, as an edict, throughout every province, was published to all the peoples, —and that the Jews be ready against that day, to avenge themselves on their enemies.
Za a ba da kofi na rubutacciyar dokar a matsayin ƙa’ida a kowane lardi, a kuma sanar wa mutanen kowace ƙasa, domin Yahudawa su zauna da shiri a ranar, domin su ɗau fansa a kan maƙiyansu.
14 The runners that rode on the swift steeds used in the king’s service, went forth, being urged forward and pressed on, by the word of the king, —and, the edict, was given in Shusan the palace.
’Yan aikan, a kan dawakan fada, suka fita a guje, umarnin sarki yana iza su. Aka kuma ba da dokar a mazaunin masarauta wadda take Shusha.
15 And, Mordecai, went forth from the presence of the king, in royal apparel, of blue and white, with a large diadem of gold, and a mantle of fine linen and purple, —and, the city Shusan, was bright and joyful.
Mordekai kuwa ya fita a gaban sarki da rigunan sarauta, masu ruwan shuɗi, da fari, da babban kambi na zinariya, da alkyabba ta lilin mai ruwan shunayya. Aka yi sowa don murna a birnin Shusha.
16 To the Jews, had come light, and joy, —and gladness and honour.
Ga Yahudawa kuwa, lokaci ne na murna da farin ciki, da jin daɗi da bangirma.
17 And, in every province, and in every city, whithersoever the word of the king and his edict did reach, joy and gladness, had the Jews, —a banquet and a happy day, —and, many from among the peoples of the land, were becoming Jews, for the dread of the Jews had fallen upon them.
A kowane lardi da kowace birni, ko’ina da dokar sarki ta kai, aka yi farin ciki a cikin Yahudawa, cike da bukukkuwa. Yawan mutane da waɗansu ƙasashe suka zama Yahudawa, don tsoron Yahudawa ya kama su.

< Esther 8 >