< Matthew 17 >

1 And after sixe dayes, Iesus tooke Peter, and Iames and Iohn his brother, and brought them vp into an hie mountaine apart,
Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus da Yakubu, da Yahaya dan'uwansa, ya kai su kan wani dutse mai tsawo su kadai.
2 And was transfigured before them: and his face did shine as the Sunne, and his clothes were as white as the light.
Kamanninsa ya canja a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, kuma rigunansa suka yi kyalli fal.
3 And beholde, there appeared vnto them Moses, and Elias, talking with him.
Sai ga Musa da Iliya sun bayyana garesu suna magana da shi.
4 Then answered Peter, and saide to Iesus, Master, it is good for vs to be here: if thou wilt, let vs make here three tabernacles, one for thee, and one for Moses, and one for Elias.
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke a wurin nan. In kana so, zan yi bukkoki uku daya dominka, daya domin Musa, daya domin Iliya.”
5 While he yet spake, behold, a bright cloude shadowed them: and beholde, there came a voyce out of the cloude, saying, This is that my beloued Sonne, in whom I am well pleased: heare him.
Sa'adda yake cikin magana, sai, girgije mai haske ya rufe su, sai murya daga girgijen, tana cewa, “Wannan kaunattacen Dana ne, shi ne wanda yake faranta mani zuciya. Ku saurare shi.”
6 And when the disciples heard that, they fell on their faces, and were sore afraide.
Da almajiran suka ji haka, suka fadi da fuskokinsu a kasa, saboda sun tsorata.
7 Then Iesus came and touched them, and said, Arise, and be not afraide.
Sai Yesu ya zo ya taba su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 And when they lifted vp their eyes, they sawe no man, saue Iesus onely.
Amma da suka daga kai ba su ga kowa ba sai Yesu kadai.
9 And as they came downe from the moutaine, Iesus charged them, saying, Shewe the vision to no man, vntil the Sonne of man rise againe from the dead.
Yayin da suke saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su, ya ce, “Kada ku fadawa kowa wannan wahayin, sai Dan Mutum ya tashi daga matattu.”
10 And his disciples asked him, saying, Why then say the Scribes that Elias must first come?
Almajiransa suka tambaye shi, suka ce, “Don me marubuta ke cewa lallai ne Iliya ya fara zuwa?”
11 And Iesus answered, and saide vnto them, Certeinely Elias must first come, and restore all thinges.
Yesu ya amsa ya ce, “Hakika, Iliya zai zo ya maido da dukan abubuwa.
12 But I say vnto you that Elias is come alreadie, and they knewe him not, but haue done vnto him whatsoeuer they would: likewise shall also the Sonne of man suffer of them.
Amma ina gaya maku, Iliya ya riga ya zo, amma ba su gane shi ba. A maimakon haka, suka yi masa abin da suka ga dama. Ta irin wanan hanya, Dan Mutum kuma zai sha wuya a hannunsu.
13 Then the disciples perceiued that he spake vnto them of Iohn Baptist.
Sa'annan almajiransa suka fahimci cewa yana yi masu magana a kan Yahaya mai Baftisma ne.
14 And when they were come to the multitude, there came to him a certaine man, and fell downe at his feete,
Da suka iso wurin taron, wani mutum ya zo gunsa, ya durkusa a gaban sa, ya ce,
15 And saide, Master, haue pitie on my sonne: for he is lunatike, and is sore vexed: for oft times he falleth into the fire, and oft times into the water.
“Ubangiji, ka ji tausayin yarona, domin yana da farfadiya, kuma yana shan wuya kwarai, domin sau da yawa yana fadawa cikin wuta ko ruwa.
16 And I brought him to thy disciples, and they could not heale him.
Na kawo shi wurin almajiran ka, amma ba su iya su warkar da shi ba.”
17 Then Iesus answered, and said, O generation faithlesse, and crooked, how long now shall I be with you! howe long nowe shall I suffer you! bring him hither to me.
Yesu ya amsa ya ce, “Marasa bangaskiya da karkataccen zamani, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan jure da ku? Ku kawo shi nan a wurina.”
18 And Iesus rebuked the deuill, and he went out of him: and the childe was healed at that houre.
Yesu ya tsauta masa, sai aljanin ya fita daga cikinsa. Yaron ya warke nan take.
19 Then came the disciples to Iesus apart, and said, Why could not we cast him out?
Sai almajiran suka zo wurin Yesu a asirce suka ce, “Me ya sa muka kasa fitar da shi?”
20 And Iesus said vnto them, Because of your vnbeliefe: for verely I say vnto you, if ye haue faith as much as is a graine of mustarde seede, ye shall say vnto this mountaine, Remooue hence to yonder place, and it shall remoue: and nothing shalbe vnpossible vnto you.
Yesu ya ce masu, “Saboda karancin bangaskiyarku. Domin hakika, ina gaya maku, in kuna da bangaskiya ko da kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan dutse, 'Matsa daga nan ka koma can,' zai kuwa matsa kuma ba abin da zai gagare ku.
21 Howbeit this kinde goeth not out, but by prayer and fasting.
[Irin wannan aljanin bashi fita sai tare da addu'a da azumi].
22 And they being in Galile, Iesus said vnto them, The Sonne of man shall be deliuered into the handes of men,
Suna zaune a Galili, Yesu ya ce wa almajiransa, “Za a bada Dan Mutum ga hannun mutane.
23 And they shall kill him, but the thirde day shall he rise againe: and they were very sorie.
Kuma za su kashe shi, a rana ta uku zai tashi.” Sai almajiransa suka yi bakin ciki kwarai.
24 And when they were come to Capernaum, they that receiued polle money, came to Peter, and sayd, Doeth not your Master pay polle money?
Da suka iso Kafarnahum, mutane masu karbar haraji na rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku na ba da rabin shekel na haraji?”
25 He sayd, Yes. And when he was come into the house, Iesus preuented him, saying, What thinkest thou, Simon? Of whome doe the Kings of the earth take tribute, or polle money? of their children, or of strangers?
Sai ya ce, “I.” Amma da Bitrus ya shiga cikin gida, Yesu ya fara magana da shi yace, “Menene tunaninka Saminu? Sarakunan duniya, daga wurin wa suke karbar haraji ko kudin fito? Daga talakawansu ko daga wurin baki?”
26 Peter sayd vnto him, Of strangers. Then said Iesus vnto him, Then are the children free.
Sai Bitrus ya ce, “Daga wurin baki,” Yesu ya ce masa, “Wato an dauke wa talakawansu biya kenan.
27 Neuerthelesse, lest we should offend them: goe to the sea, and cast in an angle, and take the first fish that commeth vp, and when thou hast opened his mouth, thou shalt finde a piece of twentie pence: that take, and giue it vnto them for me and thee.
Amma don kada mu sa masu karbar harajin su yi zunubi, ka je teku, ka jefa kugiya, ka cire kifin da ya fara zuwa. Idan ka bude bakinsa, za ka sami shekel. Ka dauke shi ka ba masu karbar harajin nawa da naka.

< Matthew 17 >