< Mark 1 >

1 The beginning of the Gospel of Iesus Christ, the Sonne of God:
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 As it is written in the Prophets, Behold, I send my messenger before thy face, which shall prepare thy way before thee.
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 The voyce of him that cryeth in the wildernesse is, Prepare the way of the Lord: make his paths straight.
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 Iohn did baptize in the wildernesse, and preach the baptisme of amendment of life, for remission of sinnes.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 And al ye countrey of Iudea, and they of Hierusalem went out vnto him, and were all baptized of him in the riuer Iordan, confessing their sinnes.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 Nowe Iohn was clothed with camels heare, and with a girdle of a skinne about his loynes: and he did eate Locusts and wilde hony,
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 And preached, saying, A stronger then I commeth after me, whose shoes latchet I am not worthy to stoupe downe, and vnloose.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 Trueth it is, I haue baptized you with water: but he will baptize you with the holy Ghost.
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 And it came to passe in those dayes, that Iesus came from Nazareth, a citie of Galile, and was baptized of Iohn in Iordan.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 And assoone as he was come out of the water, Iohn saw the heauens clouen in twaine, and the holy Ghost descending vpon him like a doue.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 Then there was a voyce from heauen, saying, Thou art my beloued Sonne, in whome I am well pleased.
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 And immediatly the Spirite driueth him into the wildernesse.
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 And he was there in the wildernesse fourtie daies, and was tempted of Satan: hee was also with the wilde beastes, and the Angels ministred vnto him.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 Now after that Iohn was committed to prison, Iesus came into Galile, preaching the Gospel of the kingdome of God,
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 And saying, The time is fulfilled, and the kingdome of God is at hand: repent and beleeue the Gospel.
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 And as he walked by the sea of Galile, he saw Simon, and Andrew his brother, casting a net into the sea, (for they were fishers.)
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 Then Iesus said vnto them, Folow me, and I will make you to be fishers of men.
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 And straightway they forsooke their nets, and folowed him.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 And when hee had gone a litle further thence, he sawe Iames the sonne of Zebedeus, and Iohn his brother, as they were in the ship, mending their nets.
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 And anon hee called them: and they left their father Zebedeus in the shippe with his hired seruants, and went their way after him.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 So they entred into Capernaum, and straightway on the Sabbath day hee entred into the Synagogue, and taught.
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 And they were astonied at his doctrine, for he taught them as one that had authoritie, and not as the Scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 And there was in their Synagogue a man in whome was an vncleane spirite, and hee cried out,
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 Saying, Ah, what haue we to do with thee, O Iesus of Nazareth? Art thou come to destroy vs? I knowe thee what thou art, euen that holy one of God.
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 And Iesus rebuked him, saying, Holde thy peace, and come out of him.
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 And the vncleane spirit tare him, and cried with a loude voyce, and came out of him.
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 And they were all amased, so that they demaunded one of another, saying, What thing is this? what newe doctrine is this? for he commandeth euen the foule spirites with authoritie, and they obey him.
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 And immediatly his fame spred abroade throughout all the region bordering on Galile.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 And assoone as they were come out of the Synagogue, they entred into the house of Symon and Andrew, with Iames and Iohn.
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 And Symons wiues mother lay sicke of a feuer, and anon they told him of her.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 And he came and tooke her by the hand, and lifted her vp, and the feuer forsooke her by and by, and shee ministred vnto them.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 And whe euen was come, at what time the sunne setteth, they brought to him all that were diseased, and them that were possessed with deuils.
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 And the whole citie was gathered together at the doore.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 And he healed many that were sicke of diuers diseases: and he cast out many deuils, and suffred not the deuils to say that they knewe him.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 And in the morning very early before day, Iesus arose and went out into a solitarie place, and there praied.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 And Simon, and they that were with him, followed carefully after him.
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 And when they had found him, they sayde vnto him, All men seeke for thee.
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 Then he said vnto them, Let vs go into the next townes, that I may preach there also: for I came out for that purpose.
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 And hee preached in their Synagogues, throughout all Galile, and cast the deuils out.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 And there came a leper to him, beseeching him, and kneeled downe vnto him, and said to him, If thou wilt, thou canst make me cleane.
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 And Iesus had compassion, and put foorth his hand, and touched him, and said to him, I wil: be thou cleane.
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 And assone as he had spoken, immediatly ye leprosie departed from him, and he was made cleane.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 And after he had giue him a streight commandement, he sent him away forthwith,
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 And sayde vnto him, See thou say nothing to any man, but get thee hence, and shewe thy selfe to the Priest, and offer for thy clensing those things, which Moses commanded, for a testimoniall vnto them.
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 But when he was departed, hee began to tel many things, and to publish the matter: so that Iesus could no more openly enter into the citie, but was without in desert places: and they came to him from euery quarter.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< Mark 1 >