< Matthew 16 >

1 Then came the Pharises and Sadduces, and did tempt him, desiring him to shew them a signe from heauen.
Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama.
2 But he answered, and said vnto them, When it is euening, ye say, Faire wether: for ye skie is red.
Amma ya amsa ya ce masu, “Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'
3 And in the morning ye say, To day shall be a tempest: for the skie is red and lowring. O hypocrites, ye can discerne the face of the skie, and can ye not discerne the signes of the times?
Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba.
4 The wicked generation, and adulterous seeketh a signe, but there shall no signe be giuen it, but that signe of the Prophet Ionas: so hee left them, and departed.
Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa.” Daga nan sai Yesu ya tafi.
5 And when his disciples were come to the other side, they had forgotten to take bread with them.
Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa,
6 Then Iesus said vnto them, Take heede and beware of the leauen of the Pharises and Sadduces.
Yesu ya ce masu, “Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa.”
7 And they reasoned among themselues, saying, It is because we haue brought no bread.
Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, “Ko saboda bamu kawo gurasa bane.”
8 But Iesus knowing it, saide vnto them, O ye of litle faith, why reason you thus among your selues, because ye haue brought no bread?
Yesu yana sane da wannan sai ya ce, “Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
9 Doe ye not yet perceiue, neither remember the fiue loaues, when there were fiue thousand men, and how many baskets tooke ye vp?
Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba?
10 Neither the seuen loaues when there were foure thousande men, and howe many baskets tooke ye vp?
Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
11 Why perceiue ye not that I said not vnto you concerning bread, that ye shoulde beware of the leauen of the Pharises and Sadduces?
Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa.”
12 Then vnderstood they that he had not said that they should beware of the leauen of bread, but of the doctrine of the Pharises, and Sadduces.
Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
13 Nowe when Iesus came into the coastes of Cesarea Philippi, hee asked his disciples, saying, Whome doe men say that I, the sonne of man am?
A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, “Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake?
14 And they said, Some say, Iohn Baptist: and some, Elias: and others, Ieremias, or one of the Prophets.
Suka ce, “Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa.”
15 He said vnto them, But whome say ye that I am?
Ya ce masu, “Amma ku wa kuke ce da ni?”
16 Then Simon Peter answered, and said, Thou art that Christ, the Sonne of the liuing God.
Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai.”
17 And Iesus answered, and saide to him, Blessed art thou, Simon, the sonne of Ionas: for flesh and blood hath not reueiled it vnto thee, but my Father which is in heauen.
Yesu ya amsa ya ce masa, “Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama.
18 And I say also vnto thee, that thou art Peter, and vpon this rocke I will builde my Church: and ye gates of hell shall not ouercome it. (Hadēs g86)
Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba. (Hadēs g86)
19 And I will giue vnto thee the keyes of the kingdome of heauen, and whatsoeuer thou shalt binde vpon earth, shalbe bound in heauen: and whatsoeuer thou shalt loose on earth, shall be loosed in heauen.
Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama,”
20 Then hee charged his disciples, that they should tell no man that he was Iesus that Christ.
Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
21 From that time foorth Iesus beganne to shewe vnto his disciples, that he must goe vnto Hierusalem, and suffer many thinges of the Elders, and of the hie Priestes, and Scribes, and be slaine, and be raised againe the thirde day.
Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku.
22 Then Peter tooke him aside, and began to rebuke him, saying, Master, pitie thy selfe: this shall not be vnto thee.
Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, “Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba.”
23 Then he turned backe, and said vnto Peter, Get thee behinde me, Satan: thou art an offence vnto me, because thou vnderstandest not the thinges that are of God, but the thinges that are of men.
Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane.”
24 Iesus then saide to his disciples, If any man will follow me, let him forsake himselfe: and take vp his crosse, and follow me.
Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni.
25 For whosoeuer will saue his life, shall lose it: and whosoeuer shall lose his life for my sake, shall finde it.
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi.
26 For what shall it profite a man though he should winne the whole worlde, if hee lose his owne soule? or what shall a man giue for recompence of his soule?
Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
27 For the Sonne of man shall come in the glory of his Father with his Angels, and then shall he giue to euery man according to his deedes.
Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa.
28 Verely I say vnto you, there bee some of them that stande here, which shall not taste of death, till they haue seene the Sonne of man come in his kingdome.
Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa.”

< Matthew 16 >