< Malachi 1 >

1 The burden of the woorde of the Lord to Israel by the ministerie of Malachi.
Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
2 I haue loued you, sayth the Lord: yet yee say, Wherein hast thou loued vs? Was not Esau Iaakobs brother, saith the Lord? yet I loued Iaakob,
“Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
3 And I hated Esau, and made his mountaines wast, and his heritage a wildernes for dragons.
amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
4 Though Edom say, wee are impouerished, but we will returne and build the desolate places, yet sayeth the Lord of hostes, they shall builde, but I will destroy it, and they shall call them, The border of wickednes, and the people, with whome the Lord is angrie for euer.
Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
5 And your eyes shall see it, and yee shall say, The Lord will be magnified vpon the border of Israel.
Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
6 A sonne honoureth his father, and a seruant his master. If then I be a father, where is mine honour? and if I be a master, where is my feare, sayth the Lord of hostes vnto you, O Priestes, that despise my Name? and yee say, Wherein haue we despised thy Name?
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
7 Ye offer vncleane bread vpon mine altar, and you say, Wherein haue we polluted thee? In that ye say the table of the Lord is not to be regarded.
“Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
8 And if yee offer the blinde for sacrifice, it is not euill: and if ye offer the lame and sicke, it is not euill: offer it nowe vnto thy prince: will he be content with thee, or accept thy person, saieth the Lord of hostes?
Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 And nowe, I pray you, pray before God, that he may haue mercie vpon vs: this hath beene by your meanes: will hee regard your persons, sayth the Lord of hostes?
“To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
10 Who is there euen among you, that would shut the doores? and kindle not fire on mine altar in vaine, I haue no pleasure in you, sayeth the Lord of hostes, neither will I accept an offering at your hande.
“Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 For from the rising of the sunne vnto the going downe of the same, my Name is great among the Gentiles, and in euery place incense shalbe offred vnto my Name, and a pure offering: for my Name is great among the heathen, sayeth the Lord of hostes.
Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 But ye haue polluted it, in that ye say, The table of the Lord is polluted and the fruit thereof, euen his meat is not to be regarded.
“Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
13 Ye said also, Beholde, it is a wearines, and ye haue snuffed at it, sayth the Lord of hostes, and ye offred that which was torne, and the lame and the sicke: thus yee offred an offring: shoulde I accept this of your hand, sayth the Lord?
Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
14 But cursed be the deceiuer, which hath in his flocke a male, and voweth, and sacrificeth vnto ye Lord a corrupt thing: for I am a great King, sayth the Lord of hostes, and my Name is terrible among the heathen.
“La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.

< Malachi 1 >