< Zechariah 1 >

1 In the eight moneth of the second yeere of Darius, came the worde of the Lord vnto Zechariah the sonne of Berechiah, the sonne of Iddo, the Prophet, saying,
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 The Lord hath bene sore displeased with your fathers.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Therefore say thou vnto them, Thus sayth the Lord of hostes, Turne ye vnto me, saith the Lord of hostes, and I will turne vnto you, saith the Lord of hostes.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Be ye not as your fathers, vnto whome the former prophets haue cried, saying, Thus sayth the Lord of hostes, Turne you nowe from your euill wayes, and from your wicked workes: but they would not heare, nor hearken vnto me, saith the Lord.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 your fathers, where are they? and doe the Prophets liue for euer?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 But did not my wordes and my statutes, which I commanded by my seruants ye Prophets, take holde of your fathers? and they returned, and sayd, As the Lord of hostes hath determined to doe vnto vs, according to our owne wayes, and according to our workes, so hath hee dealt with vs.
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 Vpon the foure and twentieth day of the eleuenth moneth, which is the moneth Shebat, in the second yeere of Darius, came the worde of the Lord vnto Zechariah the sonne of Berechiah, the sonne of Iddo the Prophet, saying,
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 I saw by night, and behold a man riding vpon a red horse, and hee stood among the mirre trees, that were in a bottome, and behinde him were there red horses speckeled and white.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 Then sayd I, O my Lord, what are these? And the Angel that talked with me, sayde vnto me, I wil shew thee what these be.
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 And the man that stood among the mirre trees, answered, and sayd, These are they whome the Lord hath sent to go through the world.
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 And they answered the Angel of the Lord, that stood among the mirre trees, and sayd, We haue gone thorowe the world: and beholde, all the world sitteth still, and is at rest.
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 Then the Angel of the Lord answered and sayd, O Lord of hostes, howe long wilt thou be vnmercifull to Ierusalem, and to the cities of Iudah, with whom thou hast bene displeased now these threescore and ten yeeres?
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 And the Lord answered the Angel that talked with me, with good wordes and comfortable wordes.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 So the Angel that communed with me, said vnto me, Crie thou, and speake, Thus saith the Lord of hostes, I am ielous ouer Ierusalem and Zion with a great zeale,
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 And am greatly angrie against the carelesse heathen: for I was angrie but a litle, and they helped forward the affliction.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Therefore thus saith the Lord, I wil returne vnto Ierusalem with tender mercie: mine house shall be builded in it, saith the Lord of hostes, and a line shall be stretched vpon Ierusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Cry yet, and speake, Thus saith the Lord of hostes, My cities shall yet be broken with plentie: the Lord shall yet comfort Zion, and shall yet chuse Ierusalem.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Then lift I vp mine eyes and sawe, and beholde, foure hornes.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 And I said vnto the Angel that talked with me, What be these? And hee answered me, These are the hornes which haue scattered Iudah, Israel, and Ierusalem.
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 And the Lord shewed me foure carpenters.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 Then said I, What come these to doe? And he answered, and said, These are the hornes, which haue scattered Iudah, so that a man durst not lift vp his head: but these are come to fray them, and to cast out the hornes of the Gentiles, which lift vp their horne ouer the land of Iudah, to scatter it.
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”

< Zechariah 1 >