< Zechariah 14 >

1 Beholde, the day of the Lord commeth, and thy spoyle shall be deuided in the middes of thee.
Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2 For I will gather all nations against Ierusalem to battell, and the citie shall be taken, and the houses spoyled, and the women defiled, and halfe of the citie shall goe into captiuitie, and the residue of the people shall not be cut off from ye citie.
Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3 Then shall the Lord goe foorth, and fight against those nations, as when he fought in the day of battell.
Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
4 And his feete shall stand in that day vpon the mount of oliues, which is before Ierusalem on the Eastside, and the mount of oliues shall cleaue in the middes thereof: toward the East and toward the West there shalbe a very great valley, and halfe of ye mountaine shall remooue toward the North, and halfe of the mountaine towarde the South.
A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
5 And yee shall flee vnto the valley of the mountaines: for the valley of the mountaines shall reache vnto Azal: yea, yee shall flee like as ye fled from the earthquake in the daies of Vzziah King of Iudah: and the Lord my God shall come, and all the Saints with thee.
Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6 And in that day shall there bee no cleare light, but darke.
A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
7 And there shall bee a day (it is knowen to the Lord) neither day nor night, but about the euening time it shall be light.
Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8 And in that day shall there waters of life goe out from Ierusalem, halfe of them towarde the East sea, and halfe of them towarde the vttermost sea, and shall be, both in sommer and winter.
A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
9 And the Lord shall bee King ouer all the earth: in that day shall there bee one Lord, and his Name shalbe one.
Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10 All the lande shall bee turned as a plaine from Geba to Rimmon, towarde the South of Ierusalem, and it shall be lifted vp, and inhabited in her place: from Beniamins gate vnto the place of the first gate, vnto the corner gate, and from the towre of Hananiel, vnto the Kings wine presses.
Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
11 And men shall dwell in it, and there shall bee no more destruction, but Ierusalem shall bee safely inhabited.
Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12 And this shall bee the plague, wherewith the Lord will smite all people, that haue fought against Ierusalem: their flesh shall consume away, though they stand vpon their feete, and their eyes shall consume in their holes, and their tongue shall consume in their mouth.
Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
13 But in that day a great tumult of the Lord shall be among them, and euery one shall take the hande of his neighbour, and his hande shall rise vp against the hand of his neighbour.
A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
14 And Iudah shall fight also against Ierusalem, and the arme of all the heathen shall be gathered rounde about, with golde and siluer, and great abundance of apparell.
Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
15 Yet this shall be the plague of the horse, of the mule, of the camell and of the asse and of all the beasts that be in these tents as this plague.
Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16 But it shall come to passe that euery one that is left of all the nations, which came against Ierusalem, shall goe vp from yere to yere to worship the King the Lord of hostes, and to keepe the feast of Tabernacles.
Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
17 And who so will not come vp of all the families of the earth vnto Ierusalem to worship the King the Lord of hostes, euen vpon them shall come no raine.
In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
18 And if the familie of Egypt goe not vp, and come not, it shall not raine vpon them. This shall be the plague wherewith the Lord will smite all the heathen, that come not vp to keepe the feast of Tabernacles.
In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
19 This shall be the punishment of Egypt, and the punishment of all the nations that come not vp to keepe the feast of Tabernacles.
Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20 In that day shall there be written vpon the bridles of the horses, The holinesse vnto the Lord, and the pottes in the Lords house shall be like the bowles before the altar.
A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
21 Yea, euery potte in Ierusalem and Iudah shall be holy vnto the Lord of hostes, and all they that sacrifice, shall come and take of them, and seethe therein: and in that day there shall be no more the Canaanite in the House of the Lord of hostes.
Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.

< Zechariah 14 >