< Judges 14 >

1 Nowe Samson went downe to Timnath, and saw a woman in Timnath of the daughters of the Philistims,
Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
2 And he came vp and told his father and his mother and saide, I haue seene a woman in Timnath of the daughters of the Philistims: now therfore giue me her to wife.
Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
3 Then his father and his mother sayde vnto him, Is there neuer a wife among the daughters of thy brethren, and among all my people, that thou must go to take a wife of the vncircumcised Philistims? And Samson sayd vnto his father, Giue mee her, for she pleaseth me well.
Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
4 But his father and his mother knewe not that it came of the Lord, that he should seeke an occasion against the Philistims: for at that time the Philistims reigned ouer Israel.
(Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
5 Then went Samson and his father and his mother downe to Timnath, and came to ye vineyardes at Timnath: and beholde, a young Lyon roared vpon him.
Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
6 And the Spirit of the Lord came vpon him, and he tare him, as one should haue rent a kid, and had nothing in his hand, neither told he his father nor his mother what he had done.
Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
7 And he went down, and talked with the woman which was beautifull in the eyes of Samson.
Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
8 And within a fewe dayes, when he returned to receiue her, he went aside to see the karkeis of the Lion: and behold, there was a swarme of bees, and hony in the body of the Lyon.
Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
9 And he tooke therof in his handes, and went eating, and came to his father and to his mother, and gaue vnto them, and they did eate: but hee told not them, that he had taken the hony out of the body of the lyon.
wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
10 So his father went down vnto the woman, and Samson made there a feast: for so vsed the yong men to doe.
To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
11 And when they sawe him, they brought thirtie companions to be with him.
Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
12 Then Samson sayd vnto them, I will nowe put forth a riddle vnto you: and if you can declare it me within seuen dayes of the feast, and finde it out, I will giue you thirty sheetes, and thirtie change of garments.
Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
13 But if you cannot declare it mee, then shall yee giue mee thirty sheetes and thirtie change of garments. And they answered him, Put forth thy riddle, that we may heare it.
In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
14 And he sayd vnto them, Out of the eater came meate, and out of the strong came sweetenesse: and they could not in three dayes expound the riddle.
Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
15 And when the seuenth day was come, they said vnto Samsons wife, Entise thine husband, that he may declare vs the riddle, lest wee burne thee and thy fathers house with fire. Haue ye called vs, to possesse vs? is it not so?
A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
16 And Samsons wife wept before him, and said, Surely thou hatest mee and louest mee not: for thou hast put forth a riddle vnto the children of my people, and hast not told it mee. And hee sayd vnto her, Beholde, I haue not told it my father, nor my mother, and shall I tell it thee?
Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
17 Then Samsons wife wept before him seuen dayes, while their feast lasted: and when the seuenth day came he tolde her, because she was importunate vpon him: so she told the riddle to the children of her people.
Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
18 And the men of ye citie sayde vnto him the seuenth day before the Sunne went downe, What is sweeter then honie? and what is stronger then a lyon? Then sayd hee vnto them, If yee had not plowed with my heiffer, yee had not found out my riddle.
Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
19 And the Spirite of the Lord came vpon him, and he went downe to Ashkelon, and slew thirtie men of them and spoyled them, and gaue chaunge of garments vnto them, which expounded the riddle: and his wrath was kindled, and he went vp to his fathers house.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
20 Then Samsons wife was giuen to his companion, whom he had vsed as his friend.
Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.

< Judges 14 >