< Judges 13 >

1 Bvt the children of Israel continued to commit wickednesse in the sight of the Lord, and the Lord deliuerd them into the handes of the Philistims fourtie yeere.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
2 Then there was a man in Zorah of the familie of the Danites, named Manoah, whose wife was baren, and bare not.
Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
3 And the Angel of the Lord appeared vnto the woman, and said vnto her, Beholde nowe, thou art baren, and bearest not: but thou shalt conceiue, and beare a sonne.
Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
4 And nowe therefore beware that thou drinke no wine, nor strong drinke, neither eate any vncleane thing.
To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
5 For loe, thou shalt conceiue and beare a sonne, and no rasor shall come on his head: for the childe shall be a Nazarite vnto God from his birth: and he shall begin to saue Israel out of the handes of the Philistims.
gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
6 Then the wife came, and tolde her husband, saying, A man of God came vnto me, and the facion of him was like the facion of the Angel of God exceeding feareful, but I asked him not whence he was, neither told he me his name,
Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
7 But he saide vnto me, Beholde, thou shalt conceiue, and beare a sonne, and nowe thou shalt drinke no wine, nor strong drinke, neither eate any vncleane thing: for the childe shalbe a Nazarite to God from his birth to the day of his death.
Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
8 Then Manoah prayed to the Lord and saide, I pray thee, my Lord, Let the man of God, whome thou sentest, come againe nowe vnto vs, and teach vs what we shall doe vnto the child when he is borne.
Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
9 And God heard the voyce of Manoah, and the Angel of God came againe vnto the wife, as she sate in the fielde, but Manoah her husband was not with her.
Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
10 And the wife made haste and ranne, and shewed her husband and sayde vnto him, Behold, the man hath appeared vnto me, that came vnto me to day.
Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
11 And Manoah arose and went after his wife, and came to the man, and saide vnto him, Art thou the man that spakest vnto the woman? and he said, Yea.
Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
12 Then Manoah sayde, Nowe let thy saying come to passe: but howe shall we order the childe and doe vnto him?
Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
13 And the Angell of the Lord saide vnto Manoah, The woman must beware of all that I said vnto her.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
14 She may eate of nothing that commeth of the vinetree: she shall not drinke wine nor strong drinke, nor eate any vncleane thing: let her obserue all that I haue commanded her.
Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
15 Manoah then said vnto the Angell of the Lord, I pray thee, let vs reteine thee, vntill we haue made readie a kid for thee.
Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
16 And the Angel of the Lord said vnto Manoah, Though thou make me abide, I will not eate of thy bread, and if thou wilt make a burnt offring, offer it vnto the Lord: for Manoah knewe not that it was an Angel of the Lord.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
17 Againe Manoah said vnto the Angell of the Lord, What is thy name, that when thy saying is come to passe, we may honour thee?
Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
18 And the Angell of the Lord saide vnto him, Why askest thou thus after my name, which is secret?
Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
19 Then Manoah tooke a kid with a meate offering, and offered it vpon a stone vnto the Lord: and the Angell did wonderously, whiles Manoah and his wife looked on.
Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
20 For when the flame came vp toward heauen from the altar, the Angel of the Lord ascended vp in the flame of the altar, and Manoah and his wife behelde it, and fell on their faces vnto the grounde.
Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
21 (So the Angel of the Lord did no more appeare vnto Manoah and his wife.) Then Manoah knewe that it was an Angel of the Lord.
Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
22 And Manoah said vnto his wife, We shall surely dye, because we haue seene God.
Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
23 But his wife saide vnto him, If the Lord woulde kill vs, he woulde not haue receiued a burnt offring, and a meate offring of our hands, neither would he haue shewed vs all these things, nor would now haue tolde vs any such.
Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
24 And the wife bare a sonne, and called his name Samson: and the childe grewe, and the Lord blessed him.
Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
25 And the Spirite of the Lord beganne to strengthen him in the host of Dan, betweene Zorah, and Eshtaol.
Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.

< Judges 13 >