< Jeremiah 9 >

1 Oh, that mine head were full of water and mine eyes a fountaine of teares, that I might weepe day and night for the slayne of the daughter of my people.
Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
2 Oh, that I had in the wildernes a cottage of wayfaring men, that I might leaue my people, and go from them: for they be all adulterers and an assembly of rebels,
Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
3 And they bende their tongues like their bowes for lyes: but they haue no courage for the trueth vpon the earth: for they proceede from euill to worse, and they haue not knowen mee, sayth the Lord.
“Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
4 Let euery one take heede of his neighbour, and trust you not in any brother: for euery brother will vse deceite, and euery friend will deale deceitfully,
“Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
5 And euery one wil deceiue his friende, and wil not speake the trueth: for they haue taught their tongues to speake lies, and take great paynes to do wickedly.
Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
6 Thine habitation is in the middes of deceiuers: because of their deceit they refuse to know me, sayth the Lord.
Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
7 Therefore thus sayth the Lord of hostes, Behold, I wil melt them, and trie them: for what should I els do for the daughter of my people?
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
8 Their tongue is as an arow shot out, and speaketh deceite: one speaketh peaceably to his neighbour with his mouth, but in his heart hee layeth waite for him.
Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
9 Shal I not visit them for these things, saith the Lord? or shall not my soule be auenged on such a nation as this?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
10 Vpon the mountaines will I take vp a weeping and a lamentation, and vpon the fayre places of the wildernes a mourning, because they are burnt vp: so that none can passe through them, neyther can men heare the voyce of the flocke: both the foule of the aire, and the beast are fled away and gone.
Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
11 And I wil make Ierusalem an heape, and a den of dragons, and I will make the cities of Iudah waste, without an inhabitant.
“Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
12 Who is wise, to vnderstande this? and to whome the mouth of the Lord hath spoken, euen he shall declare it. Why doth the land perish, and is burnt vp like a wildernesse, that none passeth through?
Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
13 And the Lord sayeth, Because they haue forsaken my Lawe, which I set before them, and haue not obeyed my voice, neither walked thereafter,
Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
14 But haue walked after the stubbernesse of their owne heart, and after Baalims, which their fathers taught them,
A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
15 Therefore thus sayth the Lord of hostes, the God of Israel, Behold, I will feede this people with wormewood, and giue them waters of gall to drinke:
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
16 I wil scatter them also among the heathen, whom neither they nor their fathers haue knowen, and I will send a sworde after them, til I haue consumed them.
Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
17 Thus sayeth the Lord of hostes, Take heede, and call for the mourning women, that they may come, and send for skilfull women that they may come,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
18 And let them make haste, and let them take vp a lamentation for vs, that our eyes may cast out teares and our eye liddes gush out of water.
Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
19 For a lamentable noyse is heard out of Zion, Howe are we destroyed, and vtterly confounded, for we haue forsaken the land, and our dwellings haue cast vs out.
An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
20 Therefore heare the worde of the Lord, O ye women, and let your eares regard the words of his mouth, and teach your daughters to mourne, and euery one her neighbour to lament.
Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
21 For death is come vp into our windowes, and is entred into our palaces, to destroy the children without, and the yong men in the streetes.
Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Speake, thus sayth the Lord, The carkeises of men shall lye, euen as the doung vpon the fielde, and as the handfull after the mower, and none shall gather them.
Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
23 Thus saith the Lord, Let not the wise man glory in his wisedome, nor the strong man glorie in his strength, neyther the riche man glorie in his riches.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
24 But let him that glorieth, glorie in this, that he vnderstandeth, and knoweth me: for I am the Lord, which shewe mercie, iudgement, and righteousnes in the earth: for in these things I delite, sayth the Lord.
amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
25 Beholde, the dayes come, sayth the Lord, that I wil visite all them, which are circumcised with the vncircumcised:
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
26 Egypt and Iudah, and Edom, and the children of Ammon, and Moab, and all the vtmost corners of them that dwell in the wildernesse: for all these nations are vncircumcised, and al the house of Israel are vncircumcised in the heart.
Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”

< Jeremiah 9 >