< Jeremiah 8 >

1 At that time, sayeth the Lord, they shall bring out the bones of the Kings of Iudah, and the bones of their princes, and the bones of the Priests and the bones of the Prophets, and the bones of the inhabitants of Ierusalem out of their graues.
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 And they shall spread them before the sunne and the moone, and all the host of heauen, whom they haue loued, and whome they haue serued, and whome they haue followed, and whome they haue sought, and whome they haue worshipped: they shall not be gathered nor be buried, but shall be as doung vpon the earth.
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 And death shall bee desired rather then life of all the residue that remaineth of this wicked familie, which remaine in all the places where I haue scattered them, sayeth the Lord of hostes.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 Thou shalt say vnto them also, Thus sayeth the Lord, Shall they fall and not arise? shall he turne away and not turne againe?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Wherefore is this people of Ierusalem turned backe by a perpetuall rebellion? they gaue themselues to deceit, and would not returne.
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 I hearkened and heard, but none spake aright: no man repented him of his wickednesse, saying, What haue I done? euery one turned to their race, as the horse rusheth into the battell.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 Euen the storke in the aire knoweth her appointed times, and the turtle and the crane and the swallowe obserue the time of their comming, but my people knoweth not the iudgement of the Lord.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 Howe doe yee say, Wee are wise, and the Lawe of the Lord is with vs? Loe, certeinly in vaine made hee it, the penne of the scribes is in vaine.
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 The wise men are ashamed: they are afraid and taken. loe, they haue reiected the word of the Lord, and what wisdome is in them?
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 Therefore will I giue their wiues vnto others, and their fieldes to them that shall possesse them: for euery one from the least euen vnto the greatest is giuen to couetousnesse, and from the Prophet euen vnto the Priest, euery one dealeth falsely.
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 For they haue healed the hurt of the daughter of my people with sweete woordes, saying, Peace, peace, when there is no peace.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 Were they ashamed when they had committed abomination? nay, they were not ashamed, neither coulde they haue any shame: therefore shall they fall among the slaine: when I shall visite them, they shall be cast downe, sayeth the Lord.
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 I wil surely consume them, sayth the Lord: there shalbe no grapes on the vine, nor figges on the figtree, and the leafe shall fade, and the things that I haue giuen them, shall depart from them.
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 Why doe we stay? assemble your selues, and let vs enter into the strong cities, and let vs be quiet there: for the Lord our God hath put vs to silence and giuen vs water with gall to drinke, because we haue sinned against the Lord.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 We looked for peace, but no good came, and for a time of health, and behold troubles.
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 The neying of his horses was heard from Dan, the whole lande trembled at the noyse of the neying of his strong horses: for they are come, and haue deuoured the land with all that is in it, the citie, and those that dwell therein.
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 For beholde, I will sende serpents, and cockatrices among you, which will not be charmed, and they shall sting you, sayth the Lord.
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 I would haue comforted my selfe against sorowe, but mine heart is heauie in me.
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 Behold, the voice of the cry of the daughter of my people for feare of them of a farre countrey, Is not the Lord in Zion? is not her king in her? Why haue they prouoked mee to anger with their grauen images, and with the vanities of a strange god?
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 The haruest is past, the sommer is ended, and we are not holpen.
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 I am sore vexed for the hurt of ye daughter of my people: I am heauie, and astonishment hath taken me.
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 Is there no balme at Gilead? is there no Physition there? Why then is not the health of the daughter of my people recouered.
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

< Jeremiah 8 >