< Isaiah 54 >

1 Rejoice, O barren that diddest not beare: breake forth into ioy and reioyce, thou that diddest not trauaile with childe: for the desolate hath moe children then the married wife, sayeth the Lord.
“Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
2 Enlarge the place of thy tents, and let them spread out the curtains of thine habitations: spare not, stretch out thy cords and make fast thy stakes.
“Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
3 For thou shalt increase on the right hande and on the left, and thy seede shall possesse the Gentiles, and dwell in the desolate cities.
Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
4 Feare not: for thou shalt not be ashamed, neither shalt thou be confounded: for thou shalt not bee put to shame: yea, thou shalt forget the shame of thy youth, and shalt not remember the reproch of thy widdowhoode any more.
“Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
5 For hee that made thee, is thine husband (whose Name is the Lord of hostes) and thy redeemer the Holy one of Israel, shall be called the God of the whole world.
Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
6 For the Lord hath called thee, being as a woman forsaken, and afflicted in spirite, and as a yong wife when thou wast refused, sayth thy God.
Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
7 For a litle while haue I forsaken thee, but with great compassion will I gather thee.
“Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
8 For a moment, in mine anger, I hid my face from thee for a litle season, but with euerlasting mercy haue I had compassion on thee, sayth the Lord thy redeemer.
Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
9 For this is vnto me as the waters of Noah: for as I haue sworne that the waters of Noah should no more goe ouer the earth, so haue I sworne that I would not be angrie with thee, nor rebuke thee.
“A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
10 For the mountaines shall remoue and the hilles shall fall downe: but my mercy shall not depart from thee, neither shall the couenant of my peace fall away, saith the Lord, that hath compassion on thee.
Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
11 O thou afflicted and tossed with tempest, that hast no comfort, beholde, I wil lay thy stones with the carbuncle, and lay thy foundation with saphirs,
“Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
12 And I will make thy windowes of emeraudes, and thy gates shining stones, and all thy borders of pleasant stones.
Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
13 And all thy children shalbe taught of the Lord, and much peace shalbe to thy children.
Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
14 In righteousnes shalt thou be established, and be farre from oppression: for thou shalt not feare it: and from feare, for it shall not come neere thee.
Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
15 Beholde, the enemie shall gather himselfe, but without me: whosoeuer shall gather himselfe in thee, against thee, shall fall.
In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
16 Beholde, I haue created the smith that bloweth the coales in the fire, and him that bringeth forth an instrument for his worke, and I haue created the destroyer to destroy.
“Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
17 But all the weapons that are made against thee, shall not prosper: and euery tongue that shall rise against thee in iudgement, thou shalt condemne. This is the heritage of the Lords seruants, and their righteousnesse is of me, sayth the Lord.
ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.

< Isaiah 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark