< Isaiah 19 >

1 The burden of Egypt. Beholde, the Lord rideth vpon a swift cloude, and shall come into Egypt, and the idoles of Egypt shall be moued at his presence, and the heart of Egypt shall melt in the middes of her.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 And I will set the Egyptians against the Egyptians: so euery one shall fight against his brother, and euery one against his neighbour, citie against citie, and kingdome against kingdome.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 And the spirite of Egypt shall faile in the middes of her, and I will destroy their counsell, and they shall seeke at the idoles, and at the sorcerers, and at them that haue spirits of diuination, and at the southsayers.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 And I will deliuer the Egyptians into the hand of the cruell Lordes, and a mightie King shall rule ouer them, sayth the Lord God of hostes.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Then the waters of the sea shall faile, and the riuers shall be dryed vp, and wasted.
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 And the riuers shall goe farre away: the riuers of defence shalbe emptied and dryed vp: the reedes and flagges shall be cut downe.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 The grasse in the riuer, and at the head of the riuers, and all that groweth by the riuer, shall wither, and be driuen away, and be no more.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 The fishers also shall mourne, and all they that cast angle into the riuer, shall lament, and they that spread their nette vpon the waters, shall be weakened.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Moreouer, they that worke in flaxe of diuers sortes, shall be confounded, and they that weaue nettes.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 For their nettes shalbe broken, and all they, that make pondes, shalbe heauie in heart.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Surely the princes of Zoan are fooles: the counsell of the wise counselers of Pharaoh is become foolish: how say ye vnto Pharaoh, I am the sonne of the wise? I am the sonne of the ancient Kings?
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Where are nowe thy wise men, that they may tell thee, or may knowe what the Lord of hostes hath determined against Egypt?
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 The princes of Zoan are become fooles: the princes of Noph are deceiued, they haue deceiued Egypt, euen the corners of the tribes thereof.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 The Lord hath mingled among them the spirite of errours: and they haue caused Egypt to erre in euery worke thereof, as a drunken man erreth in his vomite.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 Neither shall there be any worke in Egypt, which the head may doe, nor the tayle, ye branch nor the rush.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 In that day shall Egypt be like vnto women: for it shall be afraide and feare because of the moouing of the hand of the Lord of hostes, which he shaketh ouer it.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 And the land of Iudah shall be a feare vnto Egypt: euery one that maketh mention of it, shalbe afraid thereat, because of ye counsell of the Lord of hostes, which he hath determined vpon it.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 In that day shall fiue cities in the lande of Egypt speake the language of Canaan, and shall sweare by the Lord of hostes. one shall be called the citie of destruction.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 In that day shall the altar of the Lord be in the middes of the land of Egypt, and a pillar by the border thereof vnto the Lord.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 And it shall be for a signe and for a witnes vnto the Lord of hostes in the land of Egypt: for they shall crie vnto the Lord, because of the oppressers, and he shall send them a Sauiour and a great man, and shall deliuer them.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 And the Lord shall be knowen of the Egyptians, and the Egyptians shall knowe the Lord in that day, and doe sacrifice and oblation, and shall vowe vowes vnto the Lord, and performe them.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 So ye Lord shall smite Egypt, he shall smite and heale it: for he shall returne vnto ye Lord, and he shall be intreated of them and shall heale them.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 In that day shall there be a path from Egypt to Asshur, and Asshur shall come into Egypt, and Egypt into Asshur: so the Egyptians shall worship with Asshur.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 In that day shall Israel be the third with Egypt and Asshur, euen a blessing in the middes of the land.
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 For the Lord of hostes shall blesse it, saying, Blessed be my people Egypt and Asshur, the worke of mine hands, and Israel mine inheritance.
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Isaiah 19 >