< Isaiah 20 >

1 In the yeere that Tartan came to Ashdod, (when Sargon King of Asshur sent him) and had fought against Ashdod, and taken it,
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
2 At the same time spake the Lord by ye hand of Isaiah the sonne of Amoz, saying, Goe, and loose the sackecloth from thy loynes, and put off thy shooe from thy foote. And he did so, walking naked and barefoote.
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
3 And the Lord said, Like as my seruant Isaiah hath walked naked, and barefoote three yeeres, as a signe and wonder vpon Egypt, and Ethiopia,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
4 So shall the King of Asshur take away the captiuitie of Egypt, and the captiuitie of Ethiopia, both yong men and olde men, naked and barefoote, with their buttockes vncouered, to the shame of Egypt.
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
5 And they shall feare, and be ashamed of Ethiopia their expectation, and of Egypt their glory.
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
6 Then shall the inhabitant of this yle say in that day, Behold, such is our expectation, whither we fledde for helpe to be deliuered from the King of Asshur, and howe shall we be deliuered?
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”

< Isaiah 20 >