< Isaiah 55 >

1 Ho, euery one that thirsteth, come ye to the waters, and ye that haue no siluer, come, bye and eate: come, I say, bye wine and milke without siluer and without money.
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
2 Wherefore doe ye lay out siluer and not for bread? and your labour without being satisfied? hearken diligently vnto me, and eate that which is good, and let your soule delite in fatnes.
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
3 Encline your eares, and come vnto me: heare, and your soule shall liue, and I will make an euerlasting couenant with you, euen the sure mercies of Dauid.
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
4 Beholde, I gaue him for a witnes to the people, for a prince and a master vnto the people.
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
5 Beholde, thou shalt call a nation that thou knowest not, and a nation that knew not thee, shall runne vnto thee, because of the Lord thy God, and the holy one of Israel: for hee hath glorified thee.
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
6 Seeke ye the Lord while he may be found: call ye vpon him while he is neere.
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
7 Let the wicked forsake his wayes, and the vnrighteous his owne imaginations, and returne vnto the Lord, and he wil haue mercy vpon him: and to our God, for hee is very ready to forgiue.
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
8 For my thoughtes are not your thoughts, neither are your wayes my wayes, sayth the Lord.
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
9 For as ye heauens are higher then the earth, so are my wayes higher then your wayes, and my thoughtes aboue your thoughts.
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
10 Surely as the raine commeth downe and the snow from heauen, and returneth not thither, but watereth the earth and maketh it to bring forth and bud, that it may giue seede to the sower, and bread vnto him that eateth,
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
11 So shall my worde be, that goeth out of my mouth: it shall not returne vnto me voyde, but it shall accomplish that which I will, and it shall prosper in the thing whereto I sent it.
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
12 Therefore ye shall go out with ioy, and be led forth with peace: the mountaines and the hilles shall breake foorth before you into ioye, and all the trees of the fielde shall clap their handes.
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
13 For thornes there shall grow firre trees: for nettles shall growe the myrrhe tree, and it shalbe to the Lord for a name, and for an euerlasting signe that shall not be taken away.
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< Isaiah 55 >