< Isaiah 30 >

1 Wo to the rebellious children, sayth the Lord, that take counsell, but not of me, and couer with a couering, but not by my spirit, that they may lay sinne vpon sinne:
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 Which walke forth to goe downe into Egypt (and haue not asked at my mouth) to strengthen them selues with the strength of Pharaoh, and trust in the shadowe of Egypt.
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 But the strength of Pharaoh shalbe your shame, and the trust in the shadow of Egypt your confusion.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 For his princes were at Zoan, and his Ambassadours came vnto Hanes.
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 They shalbe all ashamed of the people that cannot profite them, nor helpe nor doe them good, but shalbe a shame and also a reproche.
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 The burden of the beasts of the South, in a land of trouble and anguish, from whence shall come the yong and olde lyon, the viper and fierie flying serpent against them that shall beare their riches vpon the shoulders of the coltes, and their treasures vpon the bounches of the camels, to a people that cannot profite.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 For the Egyptians are vanitie, and they shall helpe in vaine. Therefore haue I cried vnto her, Their strength is to sit still.
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Now go, and write it before them in a table, and note it in a booke that it may be for the last day for euer and euer:
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 That it is a rebellious people, lying children, and children that would not heare the law of the Lord.
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 Which say vnto the Seers, See not: and to the Prophets, Prophecie not vnto vs right things: but speake flattering things vnto vs: prophecie errours.
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 Depart out of the way: go aside out of the path: cause the holy one of Israel to cease from vs.
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 Therefoe thus saith the holy one of Israel, Because you haue cast off this worde, and trust in violence, and wickednes, and stay thereupon,
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 Therefore this iniquitie shalbe vnto you as a breach that falleth, or a swelling in an hie wall, whose breaking commeth suddenly in a moment.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 And the breaking thereof is like the breaking of a potters pot, which is broken without pitie, and in the breaking thereof is not found a sheard to take fire out of the hearth, or to take water out of the pit.
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 For thus sayd the Lord God, the Holy one of Israel, In rest and quietnes shall ye be saued: in quietnes and in confidence shall be your strength, but ye would not.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 For ye haue sayd, No, but we wil flee away vpon horses. Therefore shall ye flee. We will ride vpon the swiftest. Therefore shall your persecuters be swifter.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 A thousand as one shall flee at the rebuke of one: at the rebuke of fiue shall ye flee, till ye be left as a ship maste vpon the top of a mountaine, and as a beaken vpon an hill.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 Yet therefore will the Lord waite, that he may haue mercy vpon you, and therefore wil he be exalted, that hee may haue compassion vpon you: for the Lord is the God of iudgement. Blessed are all they that waite for him.
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Surely a people shall dwell in Zion, and in Ierusalem: thou shalt weepe no more: he wil certainly haue mercy vpon thee at the voyce of thy crye: when he heareth thee, he wil answere thee.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 And when the Lord hath giuen you the bread of aduersitie, and the water of affliction, thy raine shalbe no more kept backe, but thine eyes shall see thy raine.
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 And thine eares shall heare a worde behind thee, saying, This is the way, walke ye in it, when thou turnest to the right hand, and when thou turnest to the left.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 And ye shall pollute the couering of the images of siluer, and the riche ornament of thine images of golde, and cast them away as a menstruous cloth, and thou shalt say vnto it, Get thee hence.
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Then shall hee giue raine vnto thy seede, when thou shalt sowe the ground, and bread of the increase of the earth, and it shalbe fat and as oyle: in that day shall thy cattell be fed in large pastures.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 The oxen also and the yong asses, that till the ground, shall eate cleane prouender, which is winowed with the shoouel and with the fanne.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 And vpon euery hie mountaine, and vpon euery hie hill shall there be riuers and streames of waters, in the day of the great slaughter, when the towers shall fall.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Moreouer, the light of the moone shall be as the light of the sunne, and the light of the sunne shalbe seuen folde, and like the light of seuen dayes in the day that the Lord shall binde vp the breach of his people, and heale the stroke of their wound.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Beholde, the Name of the Lord commeth from farre, his face is burning, and the burden thereof is heauy: his lips are full of indignation, and his tongue is as a deuouring fire.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 And his spirit is as a riuer that ouerfloweth vp to the necke: it deuideth asunder, to fanne the nations with the fanne of vanitie, and there shall be a bridle to cause them to erre in the chawes of the people.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 But there shall be a song vnto you as in the night, when solemne feast is kept: and gladnes of heart, as he that commeth with a pipe to goe vnto the mount of the Lord, to the mightie one of Israel.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 And the Lord shall cause his glorious voyce to be heard, and shall declare the lighting downe of his arme with the anger of his countenance, and flame of a deuouring fire, with scattering and tempest, and hailestones.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 For with the voyce of the Lord shall Asshur be destroyed, which smote with the rod.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 And in euery place that ye staffe shall passe, it shall cleaue fast, which the Lord shall lay vpon him with tabrets and harpes: and with battels, and lifting vp of hands shall he fight against it.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 For Tophet is prepared of olde: it is euen prepared for the King: hee hath made it deepe and large: the burning thereof is fire and much wood: the breath of the Lord, like a riuer of brimstone, doeth kindle it.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Isaiah 30 >