< Isaiah 2 >

1 The worde that Isaiah the sonne of Amoz sawe vpon Iudah and Ierusalem.
Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
2 It shall be in the last dayes, that the mountaine of the house of the Lord shalbe prepared in the top of the mountaines, and shall be exalted aboue the hilles, and all nations shall flowe vnto it.
A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
3 And many people shall go, and say, Come, and let vs go vp to the mountaine of the Lord, to the house of the God of Iaakob, and hee will teach vs his wayes, and we will walke in his paths: for the Lawe shall go foorth of Zion, and the worde of the Lord from Ierusalem,
Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
4 And he shall iudge among the nations, and rebuke many people: they shall breake their swords also into mattocks, and their speares into siethes: nation shall not lift vp a sworde against nation, neither shall they learne to fight any more.
Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
5 O house of Iaakob, come ye, and let vs walke in the Lawe of the Lord.
Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
6 Surely thou hast forsaken thy people, the house of Iaakob, because they are full of the East maners, and are sorcerers as the Philistims, and abound with strange children.
Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
7 Their land also was full of siluer and golde, and there was none ende of their treasures: and their land was full of horses, and their charets were infinite.
Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
8 Their land also was full of idols: they worshipped the worke of their owne hands, which their owne fingers haue made.
Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
9 And a man bowed himselfe, and a man humbled himselfe: therefore spare them not.
Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
10 Enter into the rocke, and hide thee in the dust from before the feare of the Lord, and from the glory of his maiestie.
Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
11 The hie looke of man shall be humbled, and the loftinesse of men shalbe abased, and the Lord onely shall be exalted in that day.
Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12 For the day of the Lord of hostes is vpon all the proude and hautie, and vpon all that is exalted: and it shalbe made lowe.
Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
13 Euen vpon all the cedars of Lebanon, that are hie and exalted, and vpon all the okes of Bashan,
domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
14 And vpon all the hie mountaines, and vpon all the hilles that are lifted vp,
domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
15 And vpon euery hie tower, and vpon euery strong wall,
domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
16 And vpon all the shippes of Tarshish, and vpon all pleasant pictures.
domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
17 And the hautinesse of men shalbe brought low, and the loftinesse of men shalbe abased, and the Lord shall onely be exalted in that day.
Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
18 And the idoles will he vtterly destroy.
za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
19 Then they shall goe into the holes of the rockes, and into the caues of the earth, from before the feare of the Lord, and from the glory of his maiestie, when he shall arise to destroy the earth.
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
20 At that day shall man cast away his siluer idoles, and his golden idoles (which they had made themselues to worship them) to the mowles and to the backes,
A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
21 To goe into the holes of the rockes, and into the toppes of the ragged rockes from before the feare of the Lord, and from the glory of his maiestie, when he shall rise to destroy the earth.
Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
22 Cease you from the man whose breath is in his nostrels: for wherein is he to be esteemed?
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

< Isaiah 2 >