< Isaiah 1 >

1 A vision of Isaiah, the sonne of Amoz, which he sawe concerning Iudah and Ierusalem: in the dayes of Vzziah, Iotham, Ahaz and Hezekiah Kings of Iudah.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Heare, O heauens, and hearken, O earth: for the Lord hath sayde, I haue nourished and brought vp children, but they haue rebelled against me.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 The oxe knoweth his owner, and the asse his masters crib: but Israel hath not knowen: my people hath not vnderstand.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Ah, sinfull nation, a people laden with iniquitie: a seede of the wicked, corrupt children: they haue forsaken the Lord: they haue prouoked the holy one of Israel to anger: they are gone backewarde.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 Wherefore shoulde ye be smitten any more? for ye fall away more and more: the whole head is sicke, and the whole heart is heauie.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 From the sole of the foote vnto the head, there is nothing whole therein, but wounds, and swelling, and sores full of corruption: they haue not bene wrapped, nor bound vp, nor mollified with oyle.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Your land is waste: your cities are burnt with fire: strangers deuoure your lande in your presence, and it is desolate like the ouerthrowe of strangers.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 And the daughter of Zion shall remaine like a cotage in a vineyarde, like a lodge in a garden of cucumbers, and like a besieged citie.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 Except the Lord of hostes had reserued vnto vs, euen a small remnant: we should haue bene as Sodom, and should haue bene like vnto Gomorah.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Heare the worde of the Lord, O princes of Sodom: hearken vnto the Law of our God, O people of Gomorah.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 What haue I to doe with the multitude of your sacrifices, sayth the Lord? I am full of the burnt offerings of rams, and of the fat of fed beasts: and I desire not the blood of bullocks, nor of lambs, nor of goates.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 When ye come to appeare before me, who required this of your hands to tread in my courts?
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Bring no more oblations, in vaine: incense is an abomination vnto me: I can not suffer your newe moones, nor Sabbaths, nor solemne dayes (it is iniquitie) nor solemne assemblies.
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 My soule hateth your newe moones and your appointed feastes: they are a burden vnto me: I am weary to beare them.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 And when you shall stretch out your hands, I wil hide mine eyes from you: and though ye make many prayers, I wil not heare: for your hands are full of blood.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Wash you, make you cleane: take away the euill of your workes from before mine eyes: cease to doe euill.
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 Learne to doe well: seeke iudgement, relieue the oppressed: iudge the fatherlesse and defend the widowe.
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 Come nowe, and let vs reason together, sayth the Lord: though your sinnes were as crimsin, they shalbe made white as snowe: though they were red like skarlet, they shalbe as wooll.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 If ye consent and obey, ye shall eate the good things of the land.
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 But if ye refuse and be rebellious, ye shalbe deuoured with the sword: for the mouth of the Lord hath spoken it.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 Howe is the faithfull citie become an harlot? it was full of iudgement, and iustice lodged therein, but now they are murtherers.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Thy siluer is become drosse: thy wine is mixt with water.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Thy Princes are rebellious and companions of theeues: euery one loueth giftes, and followeth after rewards: they iudge not the fatherlesse, neither doeth the widowes cause come before them.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Therefore sayth the Lord God of hostes, the mightie one of Israel, Ah, I will ease me of mine aduersaries, and auenge me of mine enemies.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 Then I will turne mine hand vpon thee, and burne out thy drosse, till it be pure, and take away all thy tinne.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 And I will restore thy iudges as at the first, and thy counsellers as at the beginning: afterward shalt thou be called a citie of righteousnes, and a faithfull citie.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Zion shall be redeemed in iudgement, and they that returne in her, in iustice.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 And the destruction of the transgressers and of the sinners shalbe together: and they that forsake the Lord, shalbe consumed.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 For they shalbe confounded for the okes, which ye haue desired, and ye shall be ashamed of the gardens, that ye haue chosen.
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 For ye shalbe as an oke, whose leafe fadeth: and as a garden that hath no water.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 And the strong shall be as towe, and the maker thereof, as a sparke: and they shall both burne together, and none shall quench them.
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Isaiah 1 >