< Esther 3 >

1 After these things did King Ahashuerosh promote Haman the sonne of Hammedatha the Agagite, and exalted him, and set his seate aboue all the princes that were with him.
Bayan waɗannan al’amura, sai Sarki Zerzes ya girmama Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya ɗaukaka shi, ya kuma ba shi matsayi mafi girma fiye da na dukan sauran hakiman.
2 And all the Kings seruants that were at the Kings gate, bowed their knees, and reuerenced Haman: for the King had so commanded concerning him: but Mordecai bowed not the knee, neither did reuerence.
Dukan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka riƙa durƙusa suna ba wa Haman girma, gama sarki ya ba da umarni a yi masa haka. Amma Mordekai bai durƙusa ya ba shi girma ba.
3 Then the Kings seruants which were at the Kings gate, said vnto Mordecai, Why transgressest thou the Kings commandement?
Sa’an nan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka tambaye Mordekai, “Me ya sa ba ka yin biyayya da umarnin sarki?”
4 And albeit they spake dayly vnto him, yet he would not heare them: therefore they tolde Haman, that they might see how Mordecais matters would stande: for he had tolde them, that he was a Iewe.
Kowace rana suna masa magana, amma ya ƙi yă yi. Saboda haka, suka faɗa wa Haman game da wannan don su ga ko za a jure da halin Mordekai, gama ya faɗa musu cewa shi mutumin Yahuda ne.
5 And when Haman sawe that Mordecai bowed not the knee vnto him, nor did reuerence vnto him, then Haman was full of wrath.
Sa’ad da Haman ya ga cewa Mordekai ba ya durƙusa ko yă girmama shi, sai ya fusata.
6 Now he thought it too litle to lay hands onely on Mordecai: and because they had shewed him the people of Mordecai, Haman sought to destroy all the Iewes, that were throughout the whole kingdome of Ahashuerosh, euen the people of Mordecai.
Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya ga a kashe Mordekai kaɗai ba zai biya masa bukata ba. A maimakon haka, Haman ya nemi hanya a hallaka dukan mutanen Mordekai, wato, Yahudawa, a ko’ina a dukan masarautar Zerzes.
7 In the first moneth (that is the moneth Nisan) in the twelft yere of King Ahashuerosh, they cast Pur (that is a lot) before Haman, from day to day, and from moneth to moneth, vnto the twelft moneth, that is the moneth Adar.
A shekara ta goma sha biyu ta Sarki Zerzes, a wata na farko, watan Nisan, sai suka jefa fur (wato, ƙuri’a) a gaban Haman don a zaɓi rana da watan da zai dace da ƙulle-ƙullen. Sai ƙuri’a ta fāɗa a kan wata na goma sha biyu, wato, watan Adar.
8 Then Haman said vnto King Ahashuerosh, There is a people scattered, and dispersed among the people in all the prouinces of thy kingdome, and their lawes are diuers from all people, and they doe not obserue the Kings lawes: therefore it is not the Kings profite to suffer them.
Sai Haman ya ce wa Sarki Zerzes, “Akwai waɗansu mutanen da suke a warwatse, sun kuma bazu a cikin mutane cikin dukan lardunan masarautarka, waɗanda al’adunsu sun yi dabam da na dukan sauran mutane. Mutanen nan ba sa biyayya da dokokin sarki; ba zai yi wa sarki kyau a jure su ba.
9 If it please the King, let it be written that they may he destroyed, and I will pay ten thousand talents of siluer by the handes of them that haue the charge of this businesse to bring it into the Kings treasurie.
In ya gamshi sarki, bari a yi doka, don a hallaka su, zan kuma sa talenti dubu goma na azurfa a cikin ma’ajin fada saboda mutanen da suka aikata wannan sha’ani.”
10 Then the King tooke his ring from his hand and gaue it vnto Haman the sonne of Hammedatha the Agagite the Iewes aduersarie.
Saboda haka sarki ya zare zoben hatimi daga yatsarsa, ya ba wa Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban Yahudawa.
11 And the King sayde vnto Haman, Let the siluer be thine, and the people to doe with them as it pleaseth thee.
Sarki ya ce wa Haman, “Ka riƙe kuɗin, ka kuma yi da mutanen yadda ka ga dama.”
12 Then were the Kings scribes called on the thirteenth day of the first moneth, and there was written (according to all that Haman commanded) vnto the Kings officers, and to the captaines that were ouer euery prouince, and to the rulers of euery people, and to euery prouince, according to the writing thereof, and to euery people according to their language: in the name of King Ahashuerosh was it written, and sealed with the Kings ring.
Sa’an nan aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku na wata na fari. Suka rubuta dukan umarnin Haman a irin rubutun kowane lardi, kuma cikin harshen kowane mutane, zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da gwamnonin larduna dabam-dabam, da kuma hakiman mutane dabam-dabam. Aka rubuta waɗannan a sunan Sarki Zerzes da kansa, aka kuma hatimce da zobensa.
13 And the letters were sent by postes into all the Kings prouinces, to roote out, to kill and to destroy all the Iewes, both yong and olde, children and women, in one day vpon the thirteenth day of the twelft moneth, (which is the moneth Adar) and to spoyle them as a pray.
Aka aika’yan-kada-tă-kwana da saƙoni zuwa dukan lardunan sarki da umarni a hallaka, a karkashe, a kuma kawar da dukan Yahudawa, manya da ƙanana, mata da yara, a kuma washe kayayyakinsu.
14 The contents of the writing was, that there shoulde be giuen a commandement in all prouinces, and published vnto all people, that they should be ready against the same day.
Za a ba da kofin rubutun a matsayin doka a kowane lardi, a kuma sanar da mutanen kowace al’umma, domin su zauna da shiri don wannan rana.
15 And the postes compelled by the Kings commandement went forth, and the commandement was giuen in the palace at Shushan: and the King and Haman sate drinking, but the citie of Shushan was in perplexitie.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan-kada-tă-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a mazaunin masarauta da yake a Shusha. Sai Sarki da Haman suka zauna don su sha, amma birnin Shusha ya ruɗe.

< Esther 3 >