< 2 Chronicles 11 >

1 And when Rehoboam was come to Ierusalem, he gathered of the house of Iudah and Beniamin nine score thousande chosen men of warre to fight against Israel, and to bring the kingdome againe to Rehoboam.
Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
2 But the worde of the Lord came to Shemaiah the man of God, saying,
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
3 Speake vnto Rehoboam, the sonne of Salomon King of Iudah, and to all Israel that are in Iudah, and Beniamin, saying,
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
4 Thus sayth the Lord, Ye shall not goe vp, nor fight against your brethren: returne euery man to his house: for this thing is done of me. They obeyed therfore the word of the Lord, and returned from going against Ieroboam.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
5 And Rehoboam dwelt in Ierusalem, and buylt strong cities in Iudah.
Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
6 Hee buylt also Beth-lehem, and Etam, and Tekoa,
Betlehem, Etam, Tekowa,
7 And Beth-zur, and Shoco, and Adullam,
Bet-Zur, Soko, Adullam,
8 And Gath, and Maresha, and Ziph,
Gat, Maresha, Zif,
9 And Adoraim, and Lachish, and Azekah,
Adorayim, Lakish, Azeka,
10 And Zorah, and Aialon, and Hebron, which were in Iudah and Beniamin, strong cities.
Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
11 And he repaired the strong holdes and put captaines in them, and store of vitaile, and oyle and wine.
Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
12 And in all cities he put shieldes and speares, and made them exceeding strong: so Iudah and Beniamin were his.
Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
13 And the Priests and the Leuites that were in all Israel, resorted vnto him out of all their coastes.
Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
14 For the Leuites left their suburbes and their possession, and came to Iudah and to Ierusalem: for Ieroboam and his sonnes had cast them out from ministring in the Priestes office vnto the Lord.
Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
15 And he ordeyned him Priests for the hie places, and for the deuils and for the calues which he had made.
Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
16 And after the Leuites there came to Ierusalem of all the tribes of Israel, such as set their heartes to seeke the Lord God of Israel, to offer vnto the Lord God of their fathers.
Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
17 So they strengthened the kingdome of Iudah, and made Rehoboam the sonne of Salomon mightie, three yeere long: for three yeere they walked in in the way of Dauid and Salomon.
Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
18 And Rehoboam tooke him Mahalath ye daughter of Ierimoth the sonne of Dauid to wife, and Abihail the daughter of Eliab the sonne of Ishai,
Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
19 Which bare him sonnes Ieush, and Shemariah, and Zaham.
Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
20 And after her he tooke Maakah ye daughter of Absalom which bare him Abiiah, and Atthai, and Ziza, and Shelomith.
Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
21 And Rehoboam loued Maakah ye daughter of Absalom aboue all his wiues and his concubines: for he tooke eighteene wiues, and three score concubines, and begate eyght and twentie sonnes, and three score daughters.
Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
22 And Rehoboam made Abiiah the sonne of Maakah the chiefe ruler among his brethren: for he thought to make him King.
Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
23 And he taught him: and dispersed all his sonnes throughout all the countreis of Iudah and Beniamin vnto euery strong citie: and hee gaue them aboundance of vitaile, and desired many wiues.
Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.

< 2 Chronicles 11 >