< Esther 2 >

1 After these things, when the wrath of King Ahashuerosh was appeased, he remembred Vashti, and what she had done, and what was decreed against her.
Daga baya sa’ad da fushin Sarki Zerzes ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da ta yi, da kuma dokar da ya bayar game da ita.
2 And the Kings seruants that ministred vnto him, sayd, Let them seeke for the King beautifull yong virgins,
Sai masu hidimar sarki na musamman, suka kawo shawara cewa, “Bari a nemi, kyawawan budurwai saboda sarki.
3 And let the King appoynt officers through all the prouinces of his kingdome, and let them gather all the beautiful yong virgins vnto the palace of Shushan, into the house of the women, vnder the hand of Hege the Kings eunuche, keeper of the women, to giue them their things for purification.
Bari sarki yă naɗa komishinoni a kowane yanki na masarautarsa, domin su kawo dukan waɗannan kyawawan’yan mata cikin harabar mazaunin masarautar a Shusha. Bari a sa su a hannun Hegai, bābān sarki, wanda yake lura da mata, bari kuma a yi musu kulawa ta musamman.
4 And the mayde that shall please the King, let her reigne in the steade of Vashti. And this pleased the King, and he did so.
Sa’an nan bari yarinyar da ta gamshi sarki, tă zama sarauniya a maimakon Bashti.” Wannan shawara ta gamshi sarki, ya kuwa yi na’am da ita.
5 In the citie of Shushan, there was a certaine Iewe, whose name was Mordecai the sonne of Iair, the sonne of Shimei, the sonne of Kish a man of Iemini,
To, a cikin mazaunin masarauta a Shusha, akwai wani mutumin Yahuda, daga Kabilar Benyamin mai suna Mordekai, ɗan Yayir, ɗan Shimeyi, ɗan Kish,
6 Which had bene caryed away from Ierusalem with the captiuitie that was caryed away with Ieconiah King of Iudah (whom Nebuchad-nezzar King of Babel had caryed away)
wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ɗauka tare’yan zaman bauta cikin waɗanda ya ɗauko daga Urushalima, tare da Yekoniya, sarkin Yahuda.
7 And he nourished Hadassah, that is Ester, his vncles daughter: for she had neither father nor mother, and the mayde was fayre, and beautifull to looke on: and after the death of her father, and her mother, Mordecai tooke her for his own daughter
Mordekai yana da wata’yar kawunsa mai suna Hadassa, wanda ya yi reno, ba ta da mahaifi ko mahaifiya. Ita ce yarinyar da aka santa da suna Esta. Kyakkyawa ce ƙwarai. Mordekai dai ya ɗauke ta tamƙar’yarsa sa’ad da mahaifinta da mahaifiyarta suka mutu.
8 And when the Kings commandement, and his decree was published, and many maydes were brought together to the palace of Shushan, vnder the hand of Hege, Ester was brought also vnto the Kings house vnder the hande of Hege the keeper of the women.
Da aka yi shelar umarni da dokar sarki, sai aka kawo’yan mata masu yawa a mazaunin masarauta a Shusha, aka kuma sa su ƙarƙashin kulawar Hegai. Aka kawo Esta ma zuwa fadar sarki, aka danƙa ta wa Hegai, wanda yake lura da mata.
9 And the mayde pleased him, and she founde fauour in his sight: therefore he caused her things for purification to be giuen her speedily, and her state, and seuen comely maides to be giuer her out of the Kings house, and he gaue change to her and to her maydes of the best in the house of the women.
Yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashinsa. Nan da nan ya tanada mata, ya ba ta man shafawa da abinci na musamman. Ya ba ta bayi mata bakwai da aka zaɓa daga fadar sarki. Ya kuma kai ta tare da bayinta zuwa wuri mafi kyau na gidan matan kulle.
10 But Ester shewed not her people and her kinred: for Mordecai had charged her, that shee should not tell it.
Esta ba tă bayyana asalin al’ummarta da na iyalinta ba, domin Mordekai ya hana yin haka.
11 Aud Mordecai walked euery day before the court of the womens house, to knowe if Ester did well, and what should be done with her.
Kowace rana Mordekai yana kai da komowa kusa da harabar filin gidan matan kulle, domin ya san yadda Esta take, da kuma abin da yake faruwa da ita.
12 And when the course of euery mayd came, to go in to King Ahashuerosh, after that she had bene twelue moneths according to the maner of the women (for so were the dayes of their purifications accomplished, sixe moneths with oyle of myrrhe, and sixe moneths with sweete odours and in the purifying of the women:
Kafin a kai kowace yarinya wurin Sarki Zerzes, sai ta gama watanni goma sha biyu cif ana yin mata kwalliyar da aka tsara, akan ɗauki watanni shida ana shafa mata man mur, a ɗauki watanni shida kuma ana shafa mata man ƙanshi da kayan shafe-shafe.
13 And thus went the maides vnto the King) whatsoeuer she required, was giuen her, to go with her out of the womens house vnto ye kings house.
A kuma koya mata yadda za tă tafi wurin sarki. Aka ba ta duk abin da take so ta riƙe daga gidan matan kulle zuwa fadar sarki.
14 In the euening she went, and on the morow she returned into the second house of the women vnder the hand of Shaashgaz the Kings eunuche, which kept the concubines: shee came in to the King no more, except shee pleased the King, and that she were called by name.
Da yamma za tă tafi can, da safe kuma ta dawo wani ɓangaren gidan matan kullen da yake a ƙarƙashin kulawar Sha’ashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwarƙwarai. Ba ta dawowa wurin sarki sai in ta gamshe shi, sai ya kuma kira ta da suna.
15 Now when the course of Ester the daughter of Abihail the vncle of Mordecai (which had taken her as his owne daughter) came, that shee should go in to the King, she desired nothing, but what Hege the Kings eunuche the keeper of the women sayde: and Ester founde fauour in the sight of all them that looked vpon her.
Sa’ad da lokaci ya yi da Esta (yarinyar da Mordekai ya ɗauka tamƙar’yarsa,’yar kawunsa Abihayil) za tă shiga wurin sarki, ba tă nemi a ba ta kome ba in ban da abin da Hegai, bābān sarki mai lura da gidan matan kulle, ya ba da shawara. Esta kuwa ta sami tagomashin kowa da ya ganta.
16 So Ester was taken vnto King Ahashuerosh into his house royall in the tenth moneth, which is the moneth Tebeth, in the seuenth yeere of his reigne.
Aka kai Esta wurin Sarki Zerzes a mazaunin sarauta a wata na goma, watan Tebet, a shekara ta bakwai ta mulkinsa.
17 And the King loued Ester aboue all the women, and shee founde grace and fauour in his sight more then all the virgins: so that he set the crowne of the kingdome vpon her head, and made her Queene instead of Vashti.
To, sarki ya so Esta fiye da duk sauran matan, ta kuma sami tagomashinsa da kuma yardarsa fiye da duk sauran budurwai. Saboda haka ya sa rawanin sarauta a kanta, ya kuma mai da ita sarauniya a maimakon Bashti.
18 Then the King made a great feast vnto all his princes, and his seruants, which was the feast of Ester, and gaue rest vnto the prouinces, and gaue gifts, according to the power of a King.
Sarki kuwa ya yi ƙasaitacciyar liyafa, liyafar Esta, wa dukan hakimansa da shugabannin masarautarsa. Ya yi shelar hutu ko’ina a larduna, ya kuma raba kyautai a yalwace irin na sarauta.
19 And whe the virgins were gathered ye second time, then Mordecai sate in the Kings gate.
Sa’ad da aka tara budurwai karo na biyu, Mordekai kuwa yana zama a bakin ƙofar sarki.
20 Ester had not yet shewed her kindred nor her people, as Mordecai had charged her: for Ester did after the worde of Mordecai, as when she was nourished with him.
Amma Esta ta ɓoye asalin iyalinta da na al’ummarta yadda Mordekai ya ce ta yi, gama ta ci gaba da bin umarnan Mordekai yadda take yi sa’ad da yake renonta.
21 In those dayes whe Mordecai sate in the Kings gate, two of the Kings eunuches, Bigthan and Teresh, which kept the doore, were wroth, and sought to lay hand on the King Ahashuerosh.
Sa’ad da Mordekai yake zaune a bakin ƙofar sarki, sai Bigtana da Teresh, biyu daga cikin hafsoshin sarki masu gadin ƙofar shiga, suka yi fushi, suka kuma ƙulla su kashe sarki Zerzes.
22 And the thing was knowen to Mordecai, and he tolde it vnto Queene Ester, and Ester certified the King thereof in Mordecais name:
Mordekai kuwa ya sami labarin makircin, ya kuma faɗa wa Sarauniya Esta, wadda ta faɗa wa sarki, ta kuma nuna masa cewa Mordekai ne ya ji.
23 and when inquisition was made, it was found so: therefore they were both hanged on a tree: and it was written in the booke of the Chronicles before the King.
Sa’ad da aka bincika labarin aka kuma iske gaskiya ne, sai aka rataye hafsoshin nan biyu a wurin rataye mai laifi. Aka rubuta dukan wannan a cikin littafin tarihi a gaban sarki.

< Esther 2 >