< Deuteronomy 3 >

1 Then we turned, and went vp by the way of Bashan: and Og King of Bashan came out against vs, he, and all his people to fight at Edrei.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 And the Lord sayde vnto me, Feare him not, for I will deliuer him, and all his people, and his land into thine hand, and thou shalt doe vnto him as thou diddest vnto Sihon King of the Amorites, which dwelt at Heshbon.
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 So the Lord our God deliuered also vnto our hand, Og the King of Bashan, and all his people: and we smote him, vntill none was left him aliue,
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 And we tooke all his cities the same time, neither was there a citie which we tooke not from them, euen three score cities, and all ye countrey of Argob, the kingdome of Og in Bashan.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 All these cities were fenced with hie walles, gates and barres, beside vnwalled townes a great many.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 And we ouerthrewe them, as we did vnto Sihon King of Heshbon, destroying euery citie, with men, women, and children.
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 But all the cattell and the spoyle of the cities we tooke for our selues.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 Thus we tooke at that time out of the hand of two Kings of the Amorites, the land that was on this side Iorden from the riuer of Arnon vnto mount Hermon:
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 (Which Hermon the Sidonians call Shirion, but the Amorites call it Shenir)
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 All the cities of the plaine, and all Gilead, and all Bashan vnto Salchah, and Edrei, cities of the kingdome of Og in Bashan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 For onely Og King of Bashan remained of the remnant of the gyants, whose bed was a bed of yron: is it not at Rabbath among the children of Ammon? the length thereof is nine cubites, and foure cubites the breadth of it, after the cubite of a man.
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 And this land which we possessed at that time, from Aroer, which is by the riuer of Arnon, and halfe mount Gilead, and the cities thereof, gaue I vnto the Reubenites and Gadites.
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 And the rest of Gilead, and all Bashan, the kingdome of Og, gaue I vnto the halfe tribe of Manasseh: euen all the countrey of Argob with all Bashan, which is called, The land of gyants.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Iair the sonne of Manasseh tooke all the countrey of Argob, vnto the coastes of Geshuri, and of Maachathi: and called them after his owne name, Bashan, Hauoth Iair vnto this day.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 And I gaue part of Gilead vnto Machir.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 And vnto the Reubenites and Gadites I gaue the rest of Gilead, and vnto the riuer of Arnon, halfe the riuer and the borders, euen vnto the riuer Iabbok, which is the border of the children of Ammon:
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 The plaine also and Iorden, and the borders from Chinneereth euen vnto the Sea of the plaine, to wit, the salt Sea vnder the springs of Pisgah Eastwarde.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 And I commanded you the same time, saying, The Lord your God hath giuen you this lande to possesse it: ye shall goe ouer armed before your brethren the children of Israel, all men of warre.
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 Your wiues onely, and your children, and your cattel (for I know that ye haue much cattel) shall abide in your cities, which I haue giuen you,
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 Vntill the Lord haue giuen rest vnto your brethren as vnto you, and that they also possesse the lande, which the Lord your God hath giuen them beyond Iorden: then shall ye returne euery man vnto his possession, which I haue giuen you.
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 And I charged Ioshua the same time, saying, Thine eyes haue seene all that the Lord your God hath done vnto these two Kings: so shall the Lord doe vnto all the kingdomes whither thou goest.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Ye shall not feare them: for the Lord your God, he shall fight for you.
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 And I besought the Lord the same time, saying,
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 O Lord God, thou hast begunne to shewe thy seruant thy greatnesse and thy mightie hande: for where is there a God in heauen or in earth, that can do like thy workes, and like thy power?
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 I pray thee let me go ouer and see the good land that is beyond Iorden, that goodly mountaine, and Lebanon.
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 But the Lord was angrie with me for your sakes, and would not heare me: and the Lord said vnto me, Let it suffice thee, speake no more vnto me of this matter.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Get thee vp into the top of Pisgah, and lift vp thine eyes Westward, and Northwarde, and Southward, and Eastward, and behold it with thine eyes, for thou shalt not goe ouer this Iorden:
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 But charge Ioshua, and incourage him, and bolden him: for hee shall goe before this people, and he shall deuide for inheritance vnto them, the land which thou shalt see.
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 So wee abode in the valley ouer against Beth-Peor.
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.

< Deuteronomy 3 >