< Amos 3 >

1 Heare this worde that the Lord pronounceth against you, O children of Israel, euen against the whole familie which I brought vp from the land of Egypt, saying,
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 You onely haue I knowen of all the families of the earth: therefore I will visite you for all your iniquities.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Can two walke together except they bee agreed?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Will a lion roare in ye forest, when he hath no pray? or wil a lions whelpe cry out of his den, if he haue taken nothing?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Can a birde fall in a snare vpon the earth, where no fouler is? or will he take vp the snare from the earth, and haue taken nothing at all?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Or shall a trumpet be blowen in the citie, and the people be not afraide? or shall there be euil in a citie, and the Lord hath not done it?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Surely the Lord God will doe nothing, but he reueileth his secrete vnto his seruantes the Prophets.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 The lyon hath roared: who will not bee afraide? the Lord God hath spoken: who can but prophecie?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Proclayme in the palaces at Ashdod, and in the palaces in the lande of Egypt, and saye, Assemble your selues vpon the mountaines of Samaria: so beholde the great tumultes in the middes thereof, and the oppressed in the middes thereof.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 For they knowe not to doe right, sayth the Lord: they store vp violence, and robbery in their palaces.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 Therefore thus saith the Lord God, An aduersary shall come euen rounde about the countrey, and shall bring downe thy strength from thee, and thy palaces shalbe spoyled.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Thus saieth the Lord, As the shephearde taketh out of the mouth of the lyon two legges, or a piece of an eare: so shall the children of Israel be taken out that dwell in Samaria in the corner of a bed, and in Damascus, as in a couche.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Heare, and testifie in the house of Iaakob, saith the Lord God, the God of hostes.
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Surely in the day that I shall visit the transgressions of Israel vpon him, I wil also visite the altars of Beth-el, and the hornes of the altar shall be broken off, and fall to the ground.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 And I wil smite the winter house with the sommer house, and the houses of yuorie shall perish, and the great houses shalbe consumed, sayth the Lord.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >