< Amos 2 >

1 Thus sayth the Lord, For three transgressions of Moab, and for foure, I will not turne to it, because it burnt the bones of the King of Edom into lime.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
2 Therefore will I send a fire vpon Moab, and it shall deuoure the palaces of Kerioth, and Moab shall die with tumult, with shouting, and with the sound of a trumpet.
Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
3 And I will cut off the iudge out of the mids thereof, and will slay all the princes thereof with him, sayth the Lord.
Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
4 Thus saith the Lord, For three transgressions of Iudah, and for foure, I will not turne to it, because they haue cast away the Lawe of the Lord, and haue not kept his commandementes, and their lies caused them to erre after the which their fathers haue walked.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
5 Therefore will I send a fire vpon Iudah, and it shall deuoure the palaces of Ierusalem.
Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
6 Thus sayth the Lord, For three transgressions of Israel, and for foure, I will not turne to it, because they solde the righteous for siluer and the poore for shooes.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
7 They gape ouer the head of the poore, in the dust of the earth, and peruert the wayes of the meeke: and a man and his father will goe in to a mayde to dishonour mine holy Name.
Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
8 And they lye downe vpon clothes layde to pledge by euery altar: and they drinke the wine of the condemned in the house of their God.
Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
9 Yet destroyed I the Amorite before the, whose height was like the height of the cedars, and he was strong as the okes: notwithstanding I destroyed his fruite from aboue, and his roote from beneath.
“Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
10 Also I brought you vp from the land of Egypt, and led you fourtie yeres thorowe the wildernesse, to possesse the land of the Amorite.
Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
11 And I raysed vp of your sonnes for Prophets, and of your yong men for Nazarites. Is it not euen thus, O ye children of Israel, sayth the Lord?
“Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
12 But ye gaue the Nazarites wine to drinke, and commanded the Prophetes, saying, Prophecie not.
“Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
13 Behold, I am pressed vnder you as a cart is pressed that is full of sheaues.
“Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
14 Therefore the flight shall perish from the swift, and the strong shall not strengthen his force, neither shall the mightie saue his life.
Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
15 Nor he that handleth the bowe, shall stand, and he that is swift of foote, shall not escape, neyther shall he that rideth the horse, saue his life.
’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
16 And he that is of a mighty courage among the strong men, shall flee away naked in that day, sayth the Lord.
Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.

< Amos 2 >