< Amos 1 >

1 The wordes of Amos, who was among the heardmen at Tecoa, which he sawe vpon Israel, in the dayes of Vzziah king of Iudah, and in the dayes of Ieroboam the sonne of Ioash King of Israel, two yeere before the earthquake.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 And he saide, The Lord shall roare from Zion, and vtter his voyce from Ierusalem, and the dwelling places of the shepheards shall perish, and the top of Carmel shall wither,
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Thus saith the Lord, For three transgressions of Damascus, and for foure I will not turne to it, because they haue threshed Gilead with threshing instruments of yron.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 Therefore will I sende a fire into the house of Hazael, and it shall deuoure the palaces of Ben-hadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 I will breake also the barres of Damascus, and cut off the inhabitant of Bikeath-auen: and him that holdeth the scepter out of Beth-eden, and the people of Aram shall goe into captiuitie vnto Kir, sayth the Lord.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Thus sayth the Lord, For three transgressions of Azzah, and for foure, I will not turne to it, because they caried away prisoners the whole captiuitie to shut them vp in Edom.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 Therefore will I sende a fire vpon the walles of Azzah, and it shall deuoure the palaces thereof.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 And I will cut off the inhabitant from Ashdod, and him that holdeth the scepter from Ashkelon, and turne mine hande to Ekron, and the remnant of the Philistims shall perish, sayth the Lord God.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Thus sayth the Lord, For three transgressions of Tyrus, and for foure, I will not turne to it, because they shut the whole captiuitie in Edom, and haue not remembred the brotherly couenant.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 Therefore wil I send a fire vpon ye walles of Tyrus, and it shall deuoure the palaces thereof.
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Thus sayeth the Lord, For three transgressions of Edom, and for foure, I will not turne to it, because hee did pursue his brother with the sworde, and did cast off all pitie, and his anger spoyled him euermore, and his wrath watched him alway.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 Therefore will I send a fire vpon Teman, and it shall deuoure the palaces of Bozrah.
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Thus sayth ye Lord, For three transgressions of the children of Ammon, and for foure, I will not turne to it, because they haue ript vp the women with child of Gilead, that they might enlarge their border.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 Therefore will I kindle a fire in the wall of Rabbah, and it shall deuoure the palaces thereof, with shouting in the day of battell, and with a tempest in the day of the whirlewinde.
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 And their King shall go into captiuitie, he and his princes together, saith the Lord.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< Amos 1 >