< 2 Samuel 21 >

1 Then there was a famine in the dayes of Dauid, three yeeres together: and Dauid asked counsell of the Lord, and the Lord answered, It is for Saul, and for his bloodie house, because hee slewe the Gibeonites.
Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
2 Then ye King called the Gibeonites and said vnto them. (Now the Gibeonites were not of the children of Israel, but a remnant of the Amorites, vnto whom ye children of Israel had sworne: but Saul sought to slay them for his zeale toward the children of Israel and Iudah)
Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
3 And Dauid said vnto the Gibeonites, What shall I doe for you, and wherewith shall I make the atonement, that ye may blesse the inheritance of the Lord?
Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
4 The Gibeonites then answered him, Wee will haue no siluer nor golde of Saul nor of his house, neither for vs shalt thou kill any man in Israel. And he said, What ye shall say, that will I doe for you.
Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
5 Then they answered the King, The man that consumed vs and that imagined euill against vs, so that we are destroyed from remaining in any coast of Israel,
Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
6 Let seuen men of his sonnes be deliuered vnto vs, and we will hang them vp vnto the Lord in Gibeah of Saul, the Lordes chosen. And the King said, I will giue them.
a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
7 But the King had compassion on Mephibosheth the sonne of Ionathan the sonne of Saul, because of the Lordes othe, that was betweene them, euen betweene Dauid and Ionathan the sonne of Saul.
Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
8 But the King tooke the two sonnes of Rizpah the daughter of Aiah, whome shee bare vnto Saul, euen Armoni and Mephibosheth and the fiue sonnes of Michal, the daughter of Saul, whome shee bare to Adriel the sonne of Barzillai the Meholathite.
Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
9 And hee deliuered them vnto the handes of the Gibeonites, which hanged them in the mountaine before the Lord: so they died all seuen together, and they were slaine in the time of haruest: in the first dayes, and in the beginning of barly haruest.
Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
10 Then Rizpah the daughter of Aiah tooke sackecloth and hanged it vp for her vpon the rocke, from the beginning of haruest, vntill water dropped vpon them from the heauen, and suffered neither the birdes of the aire to light on the by day, nor beasts of the fielde by night.
Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
11 And it was told Dauid, what Rizpah the daughter of Aiah ye concubine of Saul had done.
Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
12 And Dauid went and tooke the bones of Saul and the bones of Ionathan his sonne from the citizens of Iabesh Gilead, which had stollen them from the streete of Beth-shan, where the Philistims had hanged them, when the Philistims had slaine Saul in Gilboa.
sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
13 So hee brought thence the bones of Saul and the bones of Ionathan his sonne, and they gathered the bones of them that were hanged.
Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
14 And the bones of Saul and of Ionathan his sonne buried they in the coutrey of Beniamin in Zelah, in the graue of Kish his father: and when they had perfourmed all that the King had commanded, God was then appeased with the land.
Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
15 Againe the Philistims had warre with Israel: and Dauid went downe, and his seruants with him, and they fought against the Philistims, and Dauid fainted.
Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
16 Then Ishi-benob which was of the sonnes of Haraphah (the head of whose speare wayed three hundreth shekels of brasse) euen he being girded with a newe sword, thought to haue slaine Dauid.
Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
17 But Abishai the sonne of Zeruiah succoured him, and smote the Philistim, and killed him. Then Dauids men sware vnto him, saying, Thou shalt goe no more out with vs to battell, lest thou quench the light of Israel.
Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
18 And after this also there was a battell with the Philistims at Gob, then Sibbechai the Hushathite slewe Saph, which was one of ye sonnes of Haraphah.
Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
19 And there was yet another battel in Gob with the Philistims, where Elhanah the sonne of Iaare-oregim, a Bethlehemite slewe Goliath the Gittite: the staffe of whose speare was like a weauers beame.
Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
20 Afterward there was also a battel in Gath, where was a man of a great stature, and had on euerie hand sixe fingers, and on euerie foote sixe toes, foure and twentie in nomber: who was also the sonne of Haraphah.
Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
21 And when hee reuiled Israel, Ionathan the sonne of Shima the brother of Dauid slewe him.
Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
22 These foure were borne to Haraphah in Gath, and died by the hande of Dauid and by the hands of his seruants.
Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.

< 2 Samuel 21 >