< 2 Samuel 20 >

1 Then there was come thither a wicked man (named Sheba the sonne of Bichri, a man of Iemini) and hee blew the trumpet, and saide, Wee haue no part in Dauid, neither haue we inheritance in the sonne of Ishai: euery man to his tents, O Israel.
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 So euery man of Israel went from Dauid and followed Sheba the sonne of Bichri: but the men of Iudah claue fast vnto their King, from Iorden euen to Ierusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 When Dauid then came to his house to Ierusalem, the King tooke the ten women his concubines, that hee had left behinde him to keepe the house, and put them in warde, and fed them, but lay no more with them: but they were enclosed vnto the day of their death, liuing in widowhode.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Then sayde the King to Amasa, Assemble me the men of Iudah within three dayes, and be thou here present.
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 So Amasa went to assemble Iudah, but hee taried longer then the time which he had appoynted him.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 Then Dauid sayd to Abishai, Now shall Sheba the sonne of Bichri doe vs more harme then did Absalom: take thou therefore thy lords seruants and follow after him, lest he get him walled cities, and escape vs.
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 And there went out after him Ioabs men, and the Cherethites and the Pelethites, and all the mightie men: and they departed out of Ierusalem, to follow after Sheba the sonne of Bichri.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 When they were at the great stone, which is in Gibeon, Amasa went before them, and Ioabs garment, that hee had put on, was girded vnto him, and vpon it was a sword girded, which hanged on his loynes in the sheath, and as hee went, it vsed to fall out.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 And Ioab sayde to Amasa, Art thou in health, my brother? and Ioab tooke Amasa by the beard with the right hand to kisse him.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 But Amasa tooke no heede to the sworde that was in Ioabs hande: for therewith he smote him in the fift rib, and shed out his bowels to the ground, and smote him not the second time: so he dyed. then Ioab and Abishai his brother followed after Sheba the sonne of Bichri.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 And one of Ioabs men stoode by him, and saide, He that fauoureth Ioab, and hee that is of Dauids part, let him go after Ioab.
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 And Amasa wallowed in blood in the mids of the way: and when the man sawe that all the people stood still, he remooued Amasa out of the way into the fielde, and cast a cloth vpon him, because he saw that euery one that came by him, stoode still.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 When hee was remoued out of the way, euerie man went after Ioab, to follow after Sheba the sonne of Bichri.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 And he went through all the tribes of Israel vnto Abel, and Bethmaachah and all places of Berim: and they gathered together, and went also after him.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 So they came, and besieged him in Abel, neere to Bethmaachah: and they cast vp a mount against the citie, and the people thereof stood on the ramper, and al the people that was with Ioab, destroyed and cast downe the wall.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 Then cried a wise woman out of the citie, Heare, heare, I pray you, say vnto Ioab, Come thou hither, that I may speake with thee.
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 And when hee came neere vnto her, the woman said, Art thou Ioab? And he answered, Yea. And she said to him, Heare the wordes of thine handmaid. And he answered, I do heare.
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 Then shee spake thus, They spake in the olde time, saying, They shoulde aske of Abel. and so haue they continued.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 I am one of them, that are peaceable and faithful in Israel: and thou goest about to destroy a citie, and a mother in Israel: why wilt thou deuoure the inheritance of the Lord?
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 And Ioab answered, and said, God forbid, God forbid it me, that I should deuoure, or destroy it.
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 The matter is not so, but a man of mout Ephraim (Sheba ye sonne of Bichri by name) hath lift vp his had against ye King, euen against Dauid: deliuer vs him onely, and I will depart from the citie. And the woman saide vnto Ioab, Beholde, his head shalbe throwen to thee ouer the wall.
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Then the woman went vnto all the people with her wisedome, and they cut off the head of Sheba the sonne of Bichri, and cast it to Ioab: the he blewe the trumpet, and they retired from the citie, euery man to his tent: and Ioab returned to Ierusalem vnto the King.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Then Ioab was ouer all the hoste of Israel, and Benaiah the sonne of Iehoiada ouer the Cherethites and ouer the Pelethies,
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 And Adoram ouer the tribute, and Ioshaphat the sonne of Ahilud the recorder,
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 And Sheia was Scribe, and Zadok and Abiathar the Priests,
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 And also Ira the Iairite was chiefe about Dauid.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< 2 Samuel 20 >