< 1 Kings 14 >

1 At that time Abiiah the sonne of Ieroboam fell sicke.
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 And Ieroboam saide vnto his wife, Vp, I pray thee, and disguise thy selfe, that they know not that thou art the wife of Ieroboam, and goe to Shiloh: for there is Ahiiah the Prophet, which tolde mee that I shoulde bee King ouer this people,
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 And take with thee tenne loaues and craknels, and a bottell of honie, and go to him: hee shall tell thee what shall become of the yong man.
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 And Ieroboams wife did so, and arose, and went to Shiloh, and came to the house of Ahiiah: but Ahiiah could not see, for his sight was decayed for his age.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Then the Lord saide vnto Ahiiah, Beholde, the wife of Ieroboam commeth to aske a thing of thee for her sonne, for he is sicke: thus and thus shalt thou say vnto her: for when shee commeth in, shee shall feine her selfe to be another.
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Therefore when Ahiiah heard the sounde of her feete as shee came in at the doore, hee saide, Come in, thou wife of Ieroboam: why feinest thou thus thy selfe to bee an other? I am sent to thee with heauie tidings.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Goe, tel Ieroboam, Thus saith the Lord God of Israel, Forasmuch as I haue exalted thee from among the people, and haue made thee prince ouer my people Israel,
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 And haue rent the kingdome away from the house of Dauid, and haue giuen it thee, and thou hast not bene as my seruant Dauid, which kept my commandements, and followed mee with all his heart, and did onely that which was right in mine eyes,
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 But hast done euil aboue al that were before thee (for thou hast gone and made thee other gods, and molten images, to prouoke me, and hast cast me behinde thy backe)
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 Therefore beholde, I will bring euill vpon the house of Ieroboam, and will cut off from Ieroboam him that pisseth against the wall, aswell him that is shut vp, as him that is left in Israel, and will sweepe away the remnant of the house of Ieroboam, as a man sweepeth away doung, till it be all gone.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 The dogges shall eate him of Ieroboams stocke that dyeth in the citie, and the foules of the aire shall eate him that dyeth in the fielde: for the Lord hath said it.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 Vp therefore and get thee to thine house: for when thy feete enter into the citie, the childe shall die.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 And al Israel shall mourne for him, and burie him: for he onely of Ieroboam shall come to the graue, because in him there is found some goodnes towarde the Lord God of Israel in the house of Ieroboam.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Moreouer, the Lord shall stirre him vp a King ouer Israel, which shall destroy the house of Ieroboam in that day: what? yea, euen nowe.
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 For the Lord shall smite Israel, as when a reede is shaken in the water, and hee shall weede Israel out of his good lad, which he gaue to their fathers, and shall scatter them beyond the Riuer, because they haue made them groues, prouoking the Lord to anger.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 And he shall giue Israel vp, because of the sinnes of Ieroboam, who did sinne, and made Israel to sinne.
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 And Ieroboams wife arose, and departed, and came to Tirzah, and when shee came to the threshold of the house, the yong man dyed,
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 And they buried him, and all Israel lamented him; according to the word of the Lord, which hee spake by the hand of his seruant Ahiiah the Prophet.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 And the rest of Ieroboams actes, how hee warred, and howe hee reigned, beholde, they are written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 And the dayes which Ieroboam reigned, were two and twentie yeere: and he slept with his fathers, and Nadab his sonne reigned in his steade.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Also Rehoboam the sonne of Salomon reigned in Iudah. Rehoboam was one and fourtie yere olde, when he began to reigne, and reigned seuenteene yere in Ierusalem, the citie which the Lord did chuse out of al the tribes of Israel, to put his Name there: and his mothers name was Naamah an Ammonite.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 And Iudah wrought wickednesse in the sight of the Lord: and they prouoked him more with their sinnes, which they had committed, then all that which their fathers had done.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 For they also made them hie places, and images, and groues on euery hie hill, and vnder euery greene tree.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 There were also Sodomites in the lande, they did according to all the abominations of the nations, which the Lord had cast out before the children of Israel.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 And in the fift yere of King Rehoboam, Shishak King of Egypt came vp against Ierusale,
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 And tooke the treasures of the house of the Lord, and the treasures of the Kings house, and tooke away all: also he caried away all the shields of golde which Salomon had made.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 And King Rehoboam made for them brasen shieldes, and committed them vnto ye hands of the chiefe of the garde, which wayted at the doore of the Kings house.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 And when the King went into the house of the Lord, the garde bare them, and brought them againe into the gard chamber.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 And the rest of the actes of Rehoboam, and all that hee did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah?
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 And there was warre betweene Rehoboam and Ieroboam continually.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 And Rehoboam slept with his fathers, and was buried with his fathers in the citie of Dauid: his mothers name was Naamah an Ammonite. And Abiiam his sonne reigned in his stead.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Kings 14 >