< 1 Kings 13 >

1 And beholde, there came a man of God out of Iudah (by the commandement of the Lord) vnto Beth-el, and Ieroboam stoode by the altar to offer incense.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 And he cryed against the altar by the comandement of the Lord, and said, O altar, altar, thus saith the Lord, Beholde, a child shalbe borne vnto the house of Dauid, Iosiah by name, and vpon thee shall he sacrifice the Priestes of the hie places that burne incense vpon thee, and they shall burne mens bones vpon thee.
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 And he gaue a signe the same time, saying, This is the signe, that the Lord hath spoken, Behold, the altar shall rent, and the ashes that are vpon it, shall fall out.
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 And when the King had heard the saying of the man of God, which he had cryed against the altar in Beth-el, Ieroboam stretched out his hand from the altar, saying, Lay holde on him: but his hande which he put foorth against him, dryed vp, and he could not pull it in againe to him.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 The altar also claue asunder, and the ashes fell out from the altar, according to the signe, which the man of God had giuen by the commandement of the Lord.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Then the King answered, and saide vnto the man of God, I beseeche thee, pray vnto ye Lord thy God, and make intercession for me, that mine hand may bee restored vnto me. And the man of God besought the Lord, and the Kings hand was restored, and became as it was afore.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 Then the King sayde vnto the man of God, Come home with mee, that thou mayest dyne, and I will giue thee a reward.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 But the man of God saide vnto the King, If thou wouldest giue me halfe thine house, I would not goe in with thee, neither woulde I eate bread nor drinke water in this place.
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 For so was it charged mee by the worde of the Lord, saying, Eate no bread nor drinke water, nor turne againe by the same way that thou camest.
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 So he went another way and returned not by the way that he came to Beth-el.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 And an olde Prophet dwelt in Beth-el, and his sonnes came and tolde him all ye woorkes, that the man of God had done that day in Beth-el, and the wordes which he had spoken vnto the King, tolde they their father.
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 And their father sayde vnto them, What way went he? and his sonnes shewed him what waye the man of God went, which came from Iudah.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 And hee saide vnto his sonnes, Saddle mee the asse. Who sadled him the asse, and hee rode thereon,
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 And went after the man of God, and found him sitting vnder an oke: and he saide vnto him, Art thou the man of God that camest from Iudah? And he sayd, Yea.
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Then he said vnto him, Come home with me, and eate bread.
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 But he answered, I may not returne with thee, nor go in with thee, neither wil I eate bread nor drinke water with thee in this place.
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 For it was charged me by the word of the Lord, saying, Thou shalt eate no bread, nor drinke water there, nor turne againe to goe by the way that thou wentest.
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 And he said vnto him, I am a Prophet also as thou art, and an Angel spake vnto me by the worde of the Lord, saying, Bring him againe with thee into thine house, that hee may eate bread and drinke water: but he lyed vnto him.
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 So he went againe with him, and did eate bread in his house, and dranke water.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 And as they sate at the table, the worde of the Lord came vnto the Prophet, that brought him againe.
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 And hee cried vnto the man of God that came from Iudah, saying, Thus sayeth the Lord, Because thou hast disobeyed the mouth of the Lord, and hast not kept the commandement which the Lord thy God commanded thee,
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 But camest backe againe, and hast eaten bread and drunke water in the place (whereof he did say vnto thee, Thou shalt eate no bread nor drinke any water) thy carkeis shall not come vnto the sepulchre of thy fathers.
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 And when he had eaten bread and drunke, he sadled him the asse, to wit, to the Prophet whome he had brought againe.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 And when hee was gone, a lion met him by the way, and slewe him, and his body was cast in the way, and the asse stoode thereby: the lion stood by the corps also.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 And beholde, men that passed by, sawe the carkeis cast in the way, and the lion standing by the corps: and they came and tolde it in ye towne where the olde Prophet dwelt.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 And when the Prophet that brought him backe againe from the waye, hearde thereof, hee sayde, It is the man of God, who hath bene disobedient vnto the commandement of the Lord: therefore the Lord hath deliuered him vnto the lion, which hath rent him and slayne him, according to the worde of the Lord, which hee spake vnto him.
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 And he spake to his sonnes, saying, Saddle me the asse. And they sadled him.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 And he went and founde his body cast in the way, and the asse and the lion stoode by the corps: and the lion had not eaten the bodie, nor torne the asse.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 And the Prophet tooke vp the body of the man of God, and layed it vpon the asse, and brought it againe, and the olde Prophet came to the citie, to lament and burie him.
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 And hee layed his bodie in his owne graue, and they lamented ouer him, saying, Alas, my brother.
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 And when he had buried him, hee spake to his sonnes, saying, When I am dead, burie ye mee also in the sepulchre, wherein the man of God is buried: lay my bones beside his bones.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 For that thing which he cried by the word of the Lord against the altar that is in Beth-el, and against all the houses of the hie places, which are in the cities of Samaria, shall surely come to passe.
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Howbeit after this, Ieroboam conuerted not from his wicked way, but turned againe, and made of the lowest of the people Priests of the hie places. Who would, might consecrate him selfe, and be of the Priestes of the hie places.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 And this thing turned to sinne vnto the house of Ieroboam, euen to roote it out, and destroy it from the face of the earth.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.

< 1 Kings 13 >