< 2 Kings 1 >

1 Then Moab rebelled against Israel after the death of Ahab:
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 And Ahaziah fell thorow the lattesse windowe in his vpper chamber which was in Samaria: so he was sicke: then he sent messengers, to whome he saide, Goe, and enquire of Baal-zebub the God of Ekron, if I shall recouer of this my disease.
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 Then the Angel of the Lord said to Eliiah the Tishbite, Arise, and goe vp to meete the messengers of the King of Samaria, and say vnto them, Is it not because there is no God in Israel, that ye goe to enquire of Baal-zebub the god of Ekron?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 Wherefore thus saith the Lord, Thou shalt not come downe from the bed on which thou art gone vp, but shalt die the death. So Eliiah departed.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 And the messengers returned vnto him, to whome he said, Why are ye nowe returned?
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 And they answered him, There came a man and met vs, and saide vnto vs, Goe, and returne vnto the King which sent you, and say vnto him, Thus saith the Lord, Is it not because there is no God in Israel, that thou sendest to enquire of Baal-zebub the God of Ekron? Therefore thou shalt not come downe from the bed, on which thou art gone vp, but shalt die ye death.
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 And he saide vnto them, What maner of man was he which came and met you, and tolde you these wordes?
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 And they said vnto him, He was an hearie man, and girded with a girdle of lether about his loynes. Then sayde he, It is Eliiah the Tishbite.
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 Therefore the King sent vnto him a captaine ouer fiftie with his fiftie men, who went vp vnto him: for beholde, he sate on the toppe of a mountaine, and he saide vnto him, O man of God, the King hath commanded that thou come downe.
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 But Eliiah answered, and saide to the captaine ouer the fiftie, If that I be a man of God, let fire come downe from the heauen, and deuoure thee and thy fiftie. So fire came downe from the heauen and deuoured him and his fiftie.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 Againe also he sent vnto him another captaine ouer fiftie, with his fiftie. Who spake, and saide vnto him, O man of God, thus the King commandeth, Come downe quickely.
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 But Eliiah answered, and saide vnto them, If I be a man of God, let fire come downe from the heauen, and deuoure thee and thy fiftie. So fire came downe from the heauen, and deuoured him and his fiftie.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 Yet againe he sent the third captaine ouer fiftie with his fiftie. And the thirde captaine ouer fiftie went vp, and came, and fell on his knees before Eliiah, and besought him, and saide vnto him, O man of God, I pray thee, let my life and the life of these thy fiftie seruants be precious in thy sight.
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Beholde, there came fire downe from the heauen and deuoured the two former captaines ouer fiftie with their fifties: therefore let my life nowe be precious in thy sight.
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 And the Angel of the Lord said vnto Eliiah, Goe downe with him, be not afraide of his presence. So he arose, and went downe with him vnto the King.
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 And he saide vnto him, Thus saith the Lord, Because thou hast sent messengers to enquire of Baal-zebub the god of Ekron, (was it not because there was no God in Israel to inquire of his worde?) therefore thou shalt not come downe off the bed, on which thou art gone vp, but shalt die the death.
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 So he dyed according to the worde of the Lord which Eliiah had spoken. And Iehoram began to reigne in his steade, in the seconde yeere of Iehoram the sonne of Iehoshaphat King of Iudah, because he had no sonne.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 Concerning the rest of the actes of Ahaziah, that he did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< 2 Kings 1 >