< 1 Kings 1 >

1 Now when King Dauid was olde, and striken in yeeres, they couered him with clothes, but no heate came vnto him.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Wherefore his seruants saide vnto him, Let there be sought for my lord ye King a yong virgin, and let her stand before the king, and cherish him: and let her lie in thy bosome, that my lord the King may get heate.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 So they sought for a faire young maide thoroughout all the coastes of Israel, and founde one Abishag a Shunamite, and brought her to the king.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 And the maid was exceeding faire, and cherished the king, and ministred to him, but the King knew her not.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Then Adoniiah the sonne of Haggith exalted himselfe, saying, I will be king. And he gate him charets and horsemen, and fiftie men to run before him.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 And his father would not displease him from his childehood, to say, Why hast thou done so? And hee was a very goodly man, and his mother bare him next after Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 And he tooke counsel of Ioab the sonne of Zeruiah, and of Abiathar the Priest: and they helped forward Adoniiah.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 But Zadok the Priest, and Benaiah the sonne of Iehoiada, and Nathan the Prophet, and Shimei, and Rei, and the men of might, which were with Dauid, were not with Adoniiah.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Then Adoniiah sacrificed sheepe and oxen, and fat cattel by the stone of Zoheleth, which is by En-rogel, and called all his brethren the kings sonnes, and al the men of Iudah ye Kings seruants,
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 But Nathan the Prophet, and Benaiah, and the mightie men, and Salomon his brother hee called not.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Wherefore Nathan spake vnto Bath-sheba the mother of Salomon, saying, Hast thou not heard, that Adoniiah ye sonne of Haggith doeth reigne, and Dauid our lord knoweth it not?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Now therefore come, and I will now giue thee counsell, howe to saue thine owne life, and the life of thy sonne Salomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Go, and get thee in vnto King Dauid, and say vnto him, Didest not thou, my lorde, O King, sweare vnto thine handmaide, saying, Assuredly Salomon thy sonne shall reigne after me, and he shall sit vpon my throne? why is then Adoniiah King?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Behold, while thou yet talkest there with the King, I also will come in after thee, and confirme thy wordes.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 So Bath-sheba went in vnto the King into the chamber, and the King was verie olde, and Abishag the Shunammite ministred vnto ye King.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 And Bath-sheba bowed and made obeisance vnto the King. And the King saide, What is thy matter?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 And shee answered him, My lorde, thou swarest by the Lord thy God vnto thine handmaide, saying, Assuredly Salomon thy sonne shall reigne after me, and he shall sit vpon my throne.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 And beholde, nowe is Adoniiah king, and now, my lord, O King, thou knowest it not.
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 And he hath offred many oxen, and fatte cattel, and sheepe, and hath called all the sonnes of the King, and Abiathar the Priest, and Ioab the captaine of the hoste: but Salomon thy seruant hath he not bidden.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 And thou, my lorde, O King, knowest that the eyes of all Israel are on thee, that thou shouldest tell them, who shoulde sit on the throne of my lord the King after him.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 For els when my lord the King shall sleepe with his fathers, I and my sonne Salomon shalbe reputed vile.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 And lo, while she yet talked with the King, Nathan also the Prophet came in.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 And they tolde the King, saying, Beholde, Nathan the Prophet. And when he was come in to the King, hee made obeisance before the King vpon his face to the ground.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 And Nathan saide, My lorde, O King, hast thou said, Adoniiah shall reigne after mee, and he shall sit vpon my throne?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 For hee is gone downe this day, and hath slaine many oxen, and fat cattel, and sheepe, and hath called al the Kings sonnes, and the captaines of the hoste, and Abiathar the Priest: and behold, they eate and drinke before him, and say, God saue King Adoniiah.
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 But me thy seruant, and Zadok the Priest, and Benaiah the sonne of Iehoiada, and thy seruant Salomon hath he not called.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Is this thing done by my lord the King, and thou hast not shewed it vnto thy seruant, who should sitte on the throne of my lorde the King after him?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Then King Dauid answered, and saide, Call me Bath-sheba. And shee came into ye Kings presence, and stoode before the King.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 And the King sware, saying, As the Lord liueth, who hath redeemed my soule out of all aduersitie,
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 That as I sware vnto thee by the Lord God of Israel, saying, Assuredly Salomon thy sonne shall reigne after me, and hee shall sit vpon my throne in my place, so will I certainely doe this day.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Then Bath-sheba bowed her face to the earth, and did reuerence vnto the King, and said, God saue my lord King Dauid for euer.
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 And King Dauid saide, Call mee Zadok the Priest, and Nathan the Prophet, and Benaiah the sonne of Iehoiada. And they came before the King.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Then the King said vnto them, Take with you the seruants of your lorde, and cause Salomon my sonne to ride vpon mine owne mule, and carie him downe to Gihon.
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 And let Zadok the Priest and Nathan the Prophet anoint him there King ouer Israel, and blowe ye the trumpet, and say, God saue king Salomon.
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Then come vp after him, that hee may come and sit vpon my throne: and hee shall bee King in my steade: for I haue appointed him to be prince ouer Israel and ouer Iudah.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Then Benaiah the sonne of Iehoiada answered the King, and said, So be it, and the Lord God of my lord the King ratifie it.
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 As the Lord hath bene with my lorde the King, so be he with Salomon, and exalt his throne aboue the throne of my lorde king Dauid.
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 So Zadok the Priest, and Nathan the Prophet, and Benaiah the sonne of Iehoiada, and the Cherethites and the Pelethites went downe and caused Salomon to ride vpon king Dauids mule, and brought him to Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 And Zadok the Priest tooke an horne of oyle out of the Tabernacle, and anointed Salomon: and they blewe the trumpet, and all the people said, God saue king Salomon.
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 And all the people came vp after him, and the people piped with pipes, and reioyced with great ioye, so that the earth rang with the sound of them.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 And Adoniiah and all the ghestes that were with him, heard it: (and they had made an ende of eating) and when Ioab heard the sound of the trumpet, he said, What meaneth this noise and vprore in the citie?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 And as he yet spake, beholde, Ionathan the sonne of Abiathar the Priest came: and Adoniiah said, Come in: for thou art a worthie man, and bringest good tidings.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 And Ionathan answered, and said to Adoniiah, Verely our lord King Dauid hath made Salomon King.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 And the King hath sent with him Zadok the Priest, and Nathan the Prophet, and Benaiah the sonne of Iehoiada, and the Cherethites, and the Pelethites, and they haue caused him to ride vpon the Kings mule.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 And Zadok the Priest, and Nathan ye Prophet haue anointed him King in Gihon: and they are gone vp from thence with ioy, and the citie is moued: this is the noise that ye haue heard.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 And Salomon also sitteth on the throne of the kingdome.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 And moreouer the Kings seruantes came to blesse our lord King Dauid, saying, God make the name of Salomon more famous then thy name, and exalt his throne aboue thy throne: therefore the King worshipped vpon the bed.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 And thus sayd the King also, Blessed bee the Lord God of Israel, who hath made one to sit on my throne this day, euen in my sight.
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Then all the ghestes that were with Adonijah, were afraide, and rose vp, and went euery man his way.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 And Adonijah fearing the presence of Salomon, arose and went, and tooke holde on the hornes of the altar.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 And one tolde Salomon, saying, Beholde, Adonijah doeth feare King Salomon: for lo, he hath caught holde on the hornes of the altar, saying, Let King Salomon sweare vnto me this day, that he will not slay his seruant with the sword.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Then Salomon sayd, If he will shewe him selfe a worthy man, there shall not an heare of him fall to the earth, but if wickednes be found in him, he shall dye.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Then King Salomon sent, and they brought him from the altar, and he came and did obeisance vnto King Salomon. And Salomon sayde vnto him, Go to thine house.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Kings 1 >