< 1 Chronicles 11 >

1 Then all Israel gathered themselues to Dauid vnto Hebron, saying, Beholde, we are thy bones and thy flesh.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 And in time past, euen when Saul was King, thou leddest Israel out and in: and the Lord thy God sayde vnto thee, Thou shalt feede my people Israel, and thou shalt be captaine ouer my people Israel.
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 So came all the Elders of Israel to the King to Hebron, and Dauid made a couenant with them in Hebron before the Lord. And they anoynted Dauid King ouer Israel, according to the word of the Lord by the hand of Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 And Dauid and all Israel went to Ierusalem, which is Iebus, where were the Iebusites, the inhabitants of the land.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 And the inhabitants of Iebus said to Dauid, Thou shalt not come in hither. Neuertheles Dauid tooke the towre of Zion, which is the city of Dauid.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 And Dauid sayd, Whosoeuer smiteth the Iebusites first, shalbe the chiefe and captaine. So Ioab the sonne of Zeruiah went first vp, and was captaine.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 And Dauid dwelt in the tower: therefore they called it the citie of Dauid.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 And he built the citie on euery side, from Millo euen round about, and Ioab repaired the rest of the citie.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 And Dauid prospered, and grewe: for the Lord of hostes was with him.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 These also are the chiefe of the valiant men that were with Dauid, and ioyned their force with him in his kingdome with al Israel, to make him King ouer Israel, according to the worde of the Lord.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 And this is the nomber of the valiant men whome Dauid had, Iashobeam the sonne of Hachmoni, the chiefe among thirtie: he lift vp his speare against three hundreth, whom he slewe at one time.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 And after him was Eleazar the sonne of Dodo the Ahohite, which was one of the three valiant men.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 He was with Dauid at Pas-dammim, and there the Philistims were gathered together to battel: and there was a parcell of ground full of barley, and the people fled before the Philistims.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 And they stood in the middes of the field, and saued it, and slewe the Philistims: so the Lord gaue a great victorie.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 And three of the thirtie captaines went to a rocke to Dauid, into the caue of Adullam. And the armie of the Philistims camped in the valley of Rephaim.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 And when Dauid was in the hold, the Philistims garison was at Beth-lehem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 And Dauid longed, and said, Oh, that one would giue me to drinke of the water of the well of Beth-lehem that is at the gate.
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Then these three brake thorowe the hoste of the Philistims, and drewe water out of the well of Beth-lehem that was by the gate, and tooke it and brought it to Dauid: but Dauid would not drinke of it, but powred it for an oblation to the Lord,
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 And said, Let not my God suffer me to do this: should I drinke the blood of these mens liues? for they haue brought it with the ieopardie of their liues: therefore he would not drinke it: these things did these three mightie men.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 And Abishai the brother of Ioab, he was chiefe of the three, and he lift vp his speare against three hundreth, and slew them, and had the name among the three.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Among the three he was more honourable then the two, and he was their captaine: but he attained not vnto the first three.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaiah the sonne of Iehoiada (the sonne of a valiant man) which had done many actes, and was of Kabzeel, he slewe two strong men of Moab: he went downe also and slewe a lion in the middes of a pit in time of snowe.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 And he slewe an Egyptian, a man of great stature, euen fiue cubites long, and in the Egyptians hand was a speare like a weauers beame: and he went downe to him with a staffe, and plucked the speare out of the Egyptians hand, and slewe him with his owne speare.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 These things did Benaiah ye sonne of Iehoiada, and had the name among the three worthies.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Behold, he was honourable among thirtie, but he attained not vnto the first three. And Dauid made him of his counsell.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 These also were valiant men of warre, Asahel the brother of Ioab, Elhanan the sonne of Dodo of Beth-lehem,
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Shammoth the Harodite, Helez the Pelonite,
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira the sonne of Ikkesh the Tekoite, Abiezer the Antothite,
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbecai the Husathite, Ilai the Ahohite,
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai the Netophathite, Heled ye sonne of Baanah the Netophathite,
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithai the sonne of Ribai of Gibeah of the children of Beniamin, Benaiah the Pirathonite,
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hurai of the riuers of Gaash, Abiel the Arbathite,
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmaueth the Baharumite, Elihaba the Shaalbonite,
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 The sonnes of Hashem the Gizonite, Ionathan the sonne of Shageh the Harite,
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam the sonne of Sacar the Hararite, Eliphal the sonne of Vr,
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hepher the Mecherathite, Ahiiah the Pelonite,
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro the Carmelite, Naarai the sonne of Ezbai,
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Ioel the brother of Nathan, Mibhar the sonne of Haggeri,
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek the Ammonite, Nahrai the Berothite, the armour bearer of Ioab, the sonne of Zeruiah,
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira the Ithrite, Garib the Ithrite,
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Vriah the Hittite, Zabad the sonne of Ahlai,
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina the sonne of Shiza the Reubenite, a captaine of the Reubenites, and thirtie with him,
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan the sonne of Maachah, and Ioshaphat the Mithnite,
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Vzia the Ashterathite, Shama and Ieiel the sonnes of Otham the Aroerite,
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Iediael the sonne of Shimri, and Ioha his brother the Tizite,
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel the Mahauite, and Ieribai and Ioshauiah the sonnes of Elnaam, and Ithmah the Moabite,
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel and Obed, and Iaasiel the Mesobaite.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chronicles 11 >