< 1 Chronicles 10 >

1 Then the Philistims fought against Israel: and the men of Israel fled before the Philistims, and fell downe slaine in mount Gilboa.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 And the Philistims pursued after Saul and after his sonnes, and the Philistims smote Ionathan, and Abinadab, and Malchishua the sonnes of Saul.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 And the battel was sore against Saul; and the archers hit him, and he was wounded of the archers.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 Then sayde Saul to his armour bearer, Drawe out thy sworde, and thrust me thorowe therewith, lest these vncircumcised come and mocke at me: but his armour bearer would not, for he was sore afraid: therefore Saul tooke the sword and fell vpon it.
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 And when his armour bearer saw that Saul was dead, he fell likewise vpon the sworde, and dyed.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 So Saul dyed and his three sonnes, and all his house, they dyed together.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 And when all the men of Israel that were in the valley, sawe how they fledde, and that Saul and his sonnes were dead, they forsooke their cities, and fled away, and the Philistims came, and dwelt in them.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 And on the morrowe when the Philistims came to spoyle them that were slaine, they found Saul and his sonnes lying in mount Gilboa.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 And when they had stript him, they tooke his head and his armour, and sent them into the land of the Philistims round about, to publish it vnto their idoles, and to the people.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 And they layd vp his armour in the house of their god, and set vp his head in the house of Dagon.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 When all they of Iabesh Gilead heard all that the Philistims had done to Saul,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 Then they arose (all the valiant men) and tooke the body of Saul, and the bodies of his sonnes, and brought them to Iabesh, and buryed the bones of them vnder an oke in Iabesh, and fasted seuen dayes.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 So Saul dyed for his transgression, that he committed against the Lord, euen against the word of the Lord, which he kept not, and in that he sought and asked counsel of a familiar spirit,
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 And asked not of the Lord: therefore he slewe him, and turned the kingdome vnto Dauid the sonne of Ishai.
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Chronicles 10 >