< Psalms 7 >

1 A Psalm of David, which he sang to the Lord because of the words of Cush, the son of Jemini. O Lord, my God, in you I have hoped. Save me from all those who persecute me, and free me:
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 lest at any time, like a lion, he might seize my soul, while there is no one to redeem me, nor any who can save.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 O Lord, my God, if there is iniquity in my hands, if I have done this:
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 if I have repaid those who rendered evils to me, may I deservedly fall away empty before my enemies:
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 let the enemy pursue my soul, and take hold of it, and trample my life into the earth, and drag down my glory into the dust. (Pause)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Rise up, Lord, in your anger. And be exalted to the borders of my enemies. And rise up, O Lord my God, according to the precept that you commanded,
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 and a congregation of people will surround you. And, because of this, return on high.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 The Lord judges the people. Judge me, O Lord, according to my justice and according to my innocence within me.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 The wickedness of sinners will be consumed, and you will direct the just: the examiner of hearts and temperaments is God.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Just is my help from the Lord, who saves the upright of heart.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 God is a just judge, strong and patient. How could he be angry throughout every day?
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Unless you will be converted, he will brandish his sword. He has extended his bow and made it ready.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 And with it, he has prepared instruments of death. He has produced his arrows for those on fire.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Behold him who has given birth to injustice: he has conceived sorrow and has begotten iniquity.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 He has opened a pit and enlarged it. And he has fallen into the hole that he made.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 His sorrow will be turned upon his own head, and his iniquity will descend upon his highest point.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 I will confess to the Lord according to his justice, and I will sing a psalm to the name of the Lord Most High.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psalms 7 >