< Psalms 6 >

1 In parts according to verses. A Psalm of David. For the octave. O Lord, do not rebuke me in your fury, nor chastise me in your anger.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Have mercy on me, Lord, for I am weak. Heal me, Lord, for my bones have become disturbed,
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 and my soul has been very troubled. But as for you, Lord, when?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Turn to me, Lord, and rescue my soul. Save me because of your mercy.
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 For there is no one in death who would be mindful of you. And who will confess to you in Hell? (Sheol h7585)
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
6 I have labored in my groaning. Every night, with my tears, I will wash my bed and drench my blanket.
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 My eye has been troubled by rage. I have grown old among all my enemies.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Scatter before me, all you who work iniquity, for the Lord has heard the voice of my weeping.
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 The Lord has heard my supplication. The Lord has accepted my prayer.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Let all my enemies be ashamed and together be greatly troubled. May they be converted and become ashamed very quickly.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.

< Psalms 6 >