< Psalms 25 >

1 Unto the end. A Psalm of David. To you, Lord, I have lifted up my soul.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 In you, my God, I trust. Let me not be put to shame.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 And do not let my enemies laugh at me. For all who remain with you will not be confounded.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 May all those who act unjustly over nothing be confounded. O Lord, demonstrate your ways to me, and teach me your paths.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Direct me in your truth, and teach me. For you are God, my Savior, and I remain with you all day long.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 O Lord, remember your compassion and your mercies, which are from ages past.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Do not remember the offenses of my youth and my ignorances. Remember me according to your mercy, because of your goodness, O Lord.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 The Lord is sweet and righteous. Because of this, he will grant a law to those who fall short in the way.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 He will direct the mild in judgment. He will teach the meek his ways.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 All the ways of the Lord are mercy and truth, to those who yearn for his covenant and his testimonies.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 Because of your name, O Lord, you will pardon my sin, for it is great.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Which is the man who fears the Lord? He has established a law for him, on the way that he has chosen.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 His soul will dwell upon good things, and his offspring will inherit the earth.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 The Lord is a firmament to those who fear him, and his covenant will be made manifest to them.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 My eyes are ever toward the Lord, for he will pull my feet from the snare.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Look upon me and have mercy on me; for I am alone and poor.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 The troubles of my heart have been multiplied. Deliver me from my needfulness.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 See my lowliness and my hardship, and release all my offenses.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Consider my enemies, for they have been multiplied, and they have hated me with an unjust hatred.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Preserve my soul and rescue me. I will not be ashamed, for I have hoped in you.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 The innocent and the righteous have adhered to me, because I have remained with you.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Free Israel, O God, from all his tribulations.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Psalms 25 >