< Numbers 9 >

1 The Lord spoke to Moses in the desert of Sinai, in the second year after they departed from the land of Egypt, in the first month, saying:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
2 “Let the sons of Israel observe the Passover at its proper time,
“Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
3 on the fourteenth day of this month, in the evening, according to all of its ceremonies and justifications.”
A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
4 And Moses instructed the sons of Israel, so that they would observe the Passover.
Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
5 And they observed it at its proper time: on the fourteenth day of the month, in the evening, at mount Sinai. The sons of Israel acted according to all the things that the Lord had commanded Moses.
suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 But behold, certain ones, who were not able to observe the Passover on that day, being unclean because of the life of a man, approaching Moses and Aaron,
Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
7 said to them: “We are unclean because of the life of a man. Why have we been cheated, in that we are not permitted to offer, at its proper time, the oblation to the Lord among the sons of Israel?”
suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
8 And Moses responded to them: “Remain, so that I may consult the Lord, as to what he will rule about you.”
Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
9 And the Lord spoke to Moses, saying:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
10 “Say to the sons of Israel: The man who becomes unclean because of a life, or if he is on a distant journey within your nation, let him observe the Passover to the Lord.
“Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
11 In the second month, on the fourteenth day of the month, in the evening, they shall eat it with unleavened bread and wild lettuce.
Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
12 They shall not leave behind any of it until morning, and they shall not break a bone of it; they shall observe all the rituals of the Passover.
Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
13 But if any man was both clean, and not on a journey, and yet he did not observe the Passover, that soul shall be exterminated from among his people, because he did not offer the sacrifice to the Lord in its time. He shall bear his sin.
Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
14 Likewise, the sojourner and the newcomer, if they are among you, shall observe the Passover to the Lord according to its ceremonies and justifications. The same precept shall be with you, as much for the newcomer as for the native.”
“‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
15 And so, on the day when the tabernacle was raised, a cloud covered it. But over the tabernacle, from evening until morning, there was, as it seemed, the appearance of fire.
A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
16 This was so continually: throughout the day a cloud covered it, and throughout the night, the appearance of fire.
Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
17 And when the cloud that was protecting the tabernacle had been taken up, then the sons of Israel advanced forward, and in the place where the cloud had remained standing, there they made camp.
Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
18 Upon the order of the Lord they advanced, and upon his order they fixed the tabernacle. All the days during which the cloud was standing over the tabernacle, they remained in the same place.
Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
19 And if it happened that it remained for a long time over it, the sons of Israel kept the night watches of the Lord, and they did not advance,
Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
20 during as many days as the cloud remained over the tabernacle. At the command of the Lord they raised their tents, and at his command they took them down.
Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
21 If the cloud remained from evening until morning, and immediately, at first light, it left the tabernacle, they set out. And if it withdrew after a day and a night, they dismantled their tents.
Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
22 Yet truly, whether it remained over the tabernacle for two days, or one month, or a longer time, the sons of Israel remained in the same place, and they did not set out. Then, as soon as it withdrew, they moved the camp.
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
23 By the word of the Lord they fixed their tents, and by his word they advanced. And they kept the night watches of the Lord, according to his command by the hand of Moses.
Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.

< Numbers 9 >