< Leviticus 25 >

1 And the Lord spoke to Moses on mount Sinai, saying:
Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai ya ce,
2 Speak to the sons of Israel, and you shall say to them: When you will have entered into the land which I will give to you, rest on the Sabbath of the Lord.
“Yi wa Isra’ilawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, dole ƙasar kanta ta kiyaye Asabbaci ga Ubangiji.
3 For six years you shall sow your field, and for six years you shall care for your vineyard, and you shall gather its fruits.
Shekara shida, za ku yi shuki, shekara shida kuma za ku aske gonakin inabinku, ku kuma tattara hatsinsu.
4 But in the seventh year, there shall be a Sabbath of the land, a resting of the Lord. You shall not sow your field, and you shall not care for your vineyard.
Amma a shekara ta bakwai, ƙasar za tă sami hutun Asabbaci, Asabbaci ga Ubangiji. Kada ku yi shuki a gonakinku, ko kuwa ku aske gonakinku na inabi.
5 What the soil shall spontaneously produce, you shall not harvest. And you shall not gather the grapes of the first-fruits as a crop. For it is a year of rest for the land.
Kada ku girbe abin da ya yi girma ba tare da ku kuka shuka ba, ko ku girbe inabin da ba ku aske ba. Ƙasar za tă kasance da shekarar hutu.
6 But these shall be yours for food, for you and for your men and women servants, and for your hired hands, and for the newcomers who sojourn with you:
Duk abin da gonar ta ba da amfani a shekara ta Asabbaci, zai zama abinci gare ku, wa kanku, bayinku maza da mata, da ma’aikatan da kuka ɗauka aiki, da kuma waɗanda ba zama ɗinɗinɗin suke yi tare da ku ba,
7 all that grows on its own shall provide food for your beasts and cattle.
haka ma zai zama abinci domin dabbobinku, da kuma namun jeji a ƙasarku. Duk abin da ƙasar ta bayar za a ci.
8 You shall also number for yourselves seven weeks of years, that is, seven times seven, which together makes forty-nine years.
“‘Ku ƙirga asabbatai bakwai na shekaru bakwai, sau bakwai. Gama asabbatai bakwai na shekaru bakwai za su yi daidai da shekaru arba’in da tara.
9 And you shall sound the trumpet in the seventh month, on the tenth day of the month, at the time of the atonement, throughout all your land.
Sa’an nan a busa ƙaho a ko’ina, a rana ta goma ga wata na bakwai; a Ranar Kafara, a busa ƙaho a dukan ƙasarku.
10 And you shall sanctify the fiftieth year, and you shall proclaim a remission for all the inhabitants of your land: for the same is the Jubilee. A man shall return to his possession, and each one shall go back to his original family,
Ku keɓe shekara ta hamsin ku kuma yi shelar’yanci a dukan ƙasar ga mazaunanta. Za tă zama shekarar murna gare ku; kowannenku zai koma ga mallakar iyalinsa, kuma kowa ga danginsa.
11 for it is the Jubilee and the fiftieth year. You shall not sow, and you shall not reap what grows in the field of its own accord, and you shall not gather the first-fruits of the crop,
Shekara ta hamsin za tă zama ta murna a gare ku; kada ku yi shuki, kada kuma ku yi girbi abin da ya yi girma da kansa, ko ku girbe inabin da ba ku lura da shi ba.
12 due to the sanctification of the Jubilee. But you shall eat them as they present themselves.
Gama shekara ce ta murna, za tă kuma zama mai tsarki a gare ku, ku dai ci abin da aka ɗauka kai tsaye daga gonaki.
13 In the year of the Jubilee, all shall return to their possessions.
“‘A wannan Shekara ta Murna, kowa zai koma ga mallakarsa.
14 When you will sell anything to your fellow citizen, or buy anything from him, do not cause your brother grief, but buy from him according to the number of years from the Jubilee,
“‘In ka sayar da gona wa wani daga mutanen ƙasarka, ko ka saya wata gona daga gare shi, kada ku cuci juna.
15 and he shall sell to you according to the computation of the produce.
Sa’ad da mutum ya sayi fili daga abokin zamansa, kuɗin zai kasance bisa ga yawan shekara hamsin ta murna da suka wuce, da kuma bisa ga yawan shekarun noma da suka rage kafin wata shekara hamsin ta murna.
16 The more years that will remain after the Jubilee, the more the price shall increase, and the less the time is numbered, so much less shall the purchase price be. For he will sell to you the time for the produce.
Idan shekarun suna da yawa, sai ku kara kuɗin filin, idan kuma shekarun ba su da yawa, sai ku rage kuɗin filin, gama ainihin abin da ake sayar maka shi ne yawan hatsin.
17 Do not be willing to afflict your countrymen, but let each one fear his God. For I am the Lord your God.
Kada ku cuci juna, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.
18 Accomplish my precepts, and observe my judgments, and complete them, so that you may be able to live in the land without any fear,
“‘Ku bi farillaina, ku kuma yi hankali ga kiyaye dokokina, za ku kuwa zauna lafiya a ƙasar.
19 and so that the soil may produce its fruits for you, from which you may eat, even to fullness, dreading violence by no one.
Sa’an nan ƙasar za tă ba da amfaninta, za ku kuwa ci ku ƙoshi, ku kuma zauna lafiya.
20 But if you will say: What shall we eat in the seventh year, if we do not sow and do not gather our produce?
Mai yiwuwa ku ce, “Me za mu ci a shekara ta bakwai in ba mu yi shuki ko girbin hatsinmu ba?”
21 I will give my blessing to you in the sixth year, and it shall yield the produce of three years.
Zan aika muku da irin albarka a shekara ta shida har da ƙasar za tă ba da amfani isashe na shekara uku.
22 And in the eighth year you shall sow, but you shall eat from the old produce, until the ninth year, until what is new matures, you shall eat what is old.
Yayinda kuke shuki a shekara ta takwas, za ku kasance da raguwa hatsi na shekarar da ta wuce, za ku kuma ci gaba da ci daga gare shi har girbin shekara ta tara yă shigo.
23 Also, the land shall not be sold in perpetuity, for it is mine, and you are newcomers and settlers to me.
“‘Kada a sayar da gona ɗinɗinɗin, gama ƙasar tawa ce, ku kuwa baƙi ne kawai, kuma’yan haya nawa.
24 Therefore, every region of your possession shall be sold under the condition of redemption.
Ko’ina a ƙasar da kuke da mallaka, dole ku tanadar da dama fansar ƙasar.
25 If your brother, being in need, will have sold his little possession and his close relative is willing, he is able to redeem what he had sold.
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta, ya kuma sayar da mallakarsa, sai danginsa na kusa yă je yă fanshi abin da mutumin ƙasarsa ya sayar.
26 But if he has no near relative, and he himself is able to find the price to redeem it,
In mutumin ba shi da wanda zai fansa masa ita, shi kansa kuwa ya wadace, ya kuma sami isashen halin fansarta,
27 the produce shall be calculated from that time when he sold it. And what is lacking, he shall repay to the buyer, and so he shall receive his possession.
sai yă lasafta yawan shekarun da aka yi tun da an sayar da filin. Kuɗin filin zai dangana ga yawan shekarun da suka rage kafin shekara hamsin ta murna da za tă zo; sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
28 But if his hand will not have discovered a way to repay the price, the buyer shall have what he bought, until the year of the Jubilee. For in that year all that has been sold shall return to the owner, and to the original possessor.
Amma in bai sami halin sāke biyansa ba, abin nan da ya sayar zai ci gaba da zama mallakar mai sayan, sai Shekara ta Murna. Za a maido masa da ita a Shekara ta Murna, sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
29 Whoever will have sold a house within the walls of a city shall have the freedom to redeem it, until one year has been completed.
“‘In mutum ya sayar da gida a birni mai katanga, yana da izini yă fanshe shi a ƙarshen shekara guda, bayan ya sayar da shi.
30 If he has not redeemed it, and the year will have turned full circle, the buyer and his posterity shall possess it, in perpetuity, and it is not able to be redeemed, even in the Jubilee.
In ba a fanshe shi a ƙarshen shekara ba, gidan da yake a birni mai katanga, zai zama mallakar na ɗinɗinɗin na mai sayan da kuma zuriyarsa. Ba za a mai da shi a Shekara ta Murna ba.
31 But if the house is in a village, which has no walls, it shall be sold by the law of the fields. If it has not been redeemed beforehand, then in the Jubilee it shall return to the owner.
Amma za a ɗauki gidaje a ƙauyuka marasa katanga kewaye da su daidai da gonaki. Za a iya fanshe su, a kuma mayar da su a Shekara ta Murna.
32 The buildings of the Levites, which are in the cities, are always able to be redeemed.
“‘Kullum, Lawiyawa suna da izini su fanshi gidajensu a biranen Lawiyawa waɗanda suka mallaka.
33 If they have not been redeemed, then in the Jubilee they shall return to the owners, for the houses of the cities of the Levites are for their possession among the sons of Israel.
Saboda haka ana iya fansa mallakar Lawiyawa, wato, gidan da aka sayar a duk birnin da yake nasu, za a kuma mayar a Shekara ta Murna, gama gidaje a biranen Lawiyawa, mallakar Isra’ilawa ne.
34 But let not their suburbs be sold, for it is an everlasting possession.
Amma kada a sayar da filayen kiwo na waɗannan birane; mallakarsu ce, ta ɗinɗinɗin.
35 If your brother has become impoverished, or infirm of hand, and you take him in, like a newcomer or a sojourner, and he lives with you,
“‘In ɗaya daga ciki mutanen ƙasarku ya talauta, ba ya kuma iya tallafa wa kansa a cikinku, sai ku taimake shi kamar yadda za ku yi da baƙo a cikinku.
36 do not accept usury from him, nor anything more than what you gave. Fear your God, so that your brother may be able to live with you.
Kada ku karɓi riba ta kowace iri daga gare shi, amma ku ji tsoron Allahnku, saboda mutumin ƙasarku yă ci gaba da zama a cikinku.
37 You shall not give him your money by usury, nor exact from him an overabundance of produce.
Kada ku ba shi rancen kuɗi da ruwa, ko ku sayar masa abinci don samun riba.
38 I am the Lord your God, who led you away from the land of Egypt, so that I might give to you the land of Canaan, and so that I may be your God.
Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, don in ba ku ƙasar Kan’ana in kuma zama Allahnku.
39 If your brother, having been compelled by poverty, will have sold himself to you, you shall not oppress him with the servitude of indentured servants.
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta a cikinku, ya kuma sayar da kansa gare ku, kada ku sa yă yi kamar bawa.
40 But he shall be like a hired hand or a settler; he shall work with you, until the year of the Jubilee.
Amma a ɗauke shi a matsayin ma’aikacin da aka ɗauka aiki, ko mazaunan da ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, sai yă yi muku aiki sai Shekara ta Murna.
41 And after that, he shall depart with his children, and he shall return to his kindred, to the possession of his fathers.
Sa’an nan a sake shi da’ya’yansa, yă kuma koma ga danginsa da mallakar kakanninsa.
42 For these are my servants, and I led them away from the land of Egypt; let them not be sold into the condition of servitude.
Gama Isra’ilawa bayina ne, waɗanda na saya daga Masar, kada a sayar da su a matsayin bayi.
43 Do not afflict him by power, but be fearful of your God.
Kada ku gwada musu azaba, amma ku ji tsoron Allahnku.
44 Let your male and female servants be from the nations which are all around you,
“‘Bayinku maza da mata, za su zo daga al’ummai da suke kewaye da ku, daga gare su za ku iya saya bayi.
45 and from the newcomers who sojourn with you, or who have been born from them in your land. These you shall have as servants,
Za ku iya saya waɗansu mutanen da ba sa zama ɗinɗinɗin a cikinku, da kuma membobin danginsu da aka haifa a ƙasarku.
46 and, by the right of inheritance, you shall transmit them to your posterity, and you shall possess them forever. But do not oppress your brothers, the sons of Israel, by power.
Za ku iya ba da su ga’ya’yanku a matsayin kayan gādo, za ku kuma iya mai da su bayi dukan rayuwarsu, amma kada ku yi mulki a bisa’yan’uwanku Isra’ilawa da tsanani.
47 If the hand of a newcomer or a sojourner will have grown strong among you, and your brother, having become impoverished, will have sold himself to him, or to any of his stock,
“‘In baƙo, ko wani da yake zama ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, ya wadace, ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku kuwa ya talauta, ya kuma sayar da kansa ga baƙon da yake zama a cikinku, ko memba na dangin baƙon,
48 after the sale, he is able to be redeemed. Whoever is willing among his brothers shall redeem him:
yana da izini samun fansa, bayan ya sayar da kansa. Ɗaya daga cikin danginsa zai iya fansarsa.
49 either the paternal uncle, or the paternal uncle’s son, or his close relative, by blood or by affinity. But if he himself will be able also, he shall redeem himself,
Kawu ko yaron ɗan’uwan mahaifin wannan mutum, ko kuwa wani dangi a cikin zuriyarsa, zai iya fanshe shi. Ko kuma in ya azurta, zai iya fansar kansa.
50 considering only the years from the time of his selling until the year of the Jubilee, and calculating the money for which he was sold, according to the number of years and the accounting of a hired hand.
Da shi da mai sayansa, za su ƙirga lokaci daga shekarar da ya sayar da kansa har zuwa Shekara ta Murna. Farashin sakinsa zai dangana a kuɗin da ake biyan ma’aikacin da aka ɗauka aiki, na yawan shekarun ne.
51 If there will have been many years which remain until the Jubilee, according to these shall he also repay the price.
In shekaru sun ragu, dole yă biya don fansarsa da kuɗi mai yawa fiye da wanda aka saye shi.
52 If few, he shall determine the accounting with him according to the number of years, and he shall repay to the buyer by what is left remaining of the years;
In shekarun sun rage kaɗan ne kafin Shekara ta Murna, sai yă yi lissafin wannan, yă kuma biya fansarsa daidai wa daida.
53 his wages being charged by what served before. He shall not afflict him violently in your sight.
Sai a yi da shi kamar ma’aikacin da aka ɗauka aiki, daga shekara zuwa shekara; dole ku tabbata mai shi bai mallake shi da tsanani ba.
54 But if, by these means, he will not be able to be redeemed, then in the year of the Jubilee he shall depart with his children.
“‘Ko ma ba a fanshe shi a ɗaya daga cikin waɗannan hanyoyi ba, sai a sake shi da’ya’yansa a Shekara ta Murna,
55 For they are my servants, the sons of Israel, whom I led away from the land of Egypt.
gama Isra’ilawa nawa ne a matsayin bayi. Su bayina ne waɗanda na saya daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.

< Leviticus 25 >