< Leviticus 24 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Instruct the sons of Israel, so that they may bring to you clear oil from the purest olives, in order to supply the lamps continuously
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 outside the veil of the testimony in the tabernacle of the covenant. And Aaron shall place these, from evening until morning, before the Lord, as a perpetual worship and ritual in your generations.
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 They shall be placed upon the most pure candlestick in the sight of the Lord always.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 You shall also receive fine wheat flour, and you shall bake twelve loaves from it, each loaf of which shall have two-tenths.
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 And you shall arrange them, six on each side, upon the most pure table before the Lord.
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 And you shall place upon them the clearest frankincense, so that the bread may be a memorial of oblation for the Lord.
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 On each Sabbath, they shall be changed before the Lord, having been received from the sons of Israel as an everlasting covenant.
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 And they shall be for Aaron and his sons, so that they may eat these in the holy place; for it is the Holy of holies from the sacrifices of the Lord, as a perpetual right.
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 Then, behold, the son of an Israelite woman, whom she had born of an Egyptian man among the sons of Israel, going out, was quarreling in the camp with a man of Israel.
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 And when he had blasphemed the name, and had cursed it, he was led to Moses. (Now his mother was called Shelomith, the daughter of Dibri from the tribe of Dan.)
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 And they sent him to prison, until they might know what the Lord would command,
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 who spoke to Moses,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 saying: Lead away the blasphemer beyond the camp, and let all who heard him place their hands upon his head, and let the entire people stone him.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 And you shall say to the sons of Israel: The man who curses his God shall bear his sin,
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 and whoever will have blasphemed the name of the Lord shall be put to death. The entire multitude shall overwhelm him with stones, whether he be a citizen or a sojourner. Whoever blasphemes the name of the Lord shall be put to death.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 Whoever will have struck and killed a man shall be put to death.
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 Whoever will have struck down an animal shall repay its equivalent, that is, a life for a life.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 Whoever will have inflicted a blemish on any of his citizens, just as he has done, so shall it be done to him:
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 fracture for fracture, eye for eye, tooth for tooth, shall he repay. Whatever degree of blemish he has inflicted, so shall he be compelled to suffer.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 Whoever strikes down a beast, shall repay another. Whoever strikes a man shall be punished.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 Let there be equal judgment among you, whether it is a sojourner or a citizen who will have sinned. For I am the Lord your God.
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 And Moses spoke to the sons of Israel. And they led away him who had blasphemed, beyond the camp, and they overwhelmed him with stones. And the sons of Israel did just as the Lord had instructed Moses.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Leviticus 24 >