< Numbers 23 >

1 And Balaam said to Balak, “Build seven altars here for me, and prepare as many calves, and the same number of rams.”
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
2 And when he had acted according to the words of Balaam, they placed a calf and a ram together on each altar.
Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
3 And Balaam said to Balak: “Stand for a little while next to your holocaust, until I go, to see if perhaps the Lord will meet with me. And whatever he will command, I shall speak to you.”
Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
4 And after he had quickly departed, God met with him. And Balaam, speaking to him, said: “I have set up seven altars, and I have placed a calf and a ram on each.”
Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
5 Then the Lord placed the word in his mouth, and he said: “Return to Balak, and you shall say this.”
Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
6 Returning, he found Balak standing next to his holocaust, with all the leaders of the Moabites.
Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
7 And taking up his parable, he said: “Balak, king of the Moabites, has led me from Aram, from the mountains of the east. ‘Come forth,’ he said, ‘and curse Jacob. Hurry and condemn Israel.’
Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
8 How shall I curse him, whom God has not cursed? For what reason would I condemn him, whom the Lord does not condemn?
Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
9 I will look upon him from the tops of the stones, and I will consider him from the hills. This people shall dwell alone, and they shall not be counted among the nations.
Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
10 Who can number the dust that is Jacob, and who can know the number of the stock of Israel? May my soul die a just death, and may my end be like theirs.”
Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
11 And Balak said to Balaam: “What is this that you are doing? I called for you, in order to curse my enemies, and to the contrary, you bless them.”
Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
12 He answered him, “How can I say anything other than what the Lord orders?”
Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
13 Therefore, Balak said: “Come with me to another place, from where you may see a portion of Israel, though you cannot see them all. Curse them from there.”
Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
14 And when he had led him to a lofty place, on the top of mount Pisgah, Balaam built seven altars, and placing upon each a calf and a ram,
Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
15 he said to Balak, “Stand here next to your holocaust, while I continue on to meet him.”
Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
16 And when the Lord had met him, and had put the word in his mouth, he said, “Return to Balak, and you shall say this to him.”
Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
17 Returning, he found him standing next to his holocaust, and the leaders of the Moabites were with him. And Balak said to him, “What has the Lord spoken?”
Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
18 But, taking up his parable, he said: “Stand, Balak, and pay attention. Listen, you son of Zippor.
Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
19 God is not like a man, so that he would lie, nor is he like a son of man, so that he would be changed. Therefore, having spoken, will he not act? Has he ever spoken, and not fulfilled?
Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
20 I was led here to bless, and I have no strength to hinder the blessing.
Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
21 There is no idol in Jacob; neither is there a false image to be seen in Israel. The Lord his God is with him, and the resound of royal victory is in him.
“Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
22 God has led him away from Egypt; his strength is like that of the rhinoceros.
Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
23 There is no soothsaying in Jacob, nor any divination in Israel. In their times, it shall be told to Jacob and to Israel what God has wrought.
Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
24 Behold, the people will rise up like a lioness, and lie down like a lion. But they will not lie down until they devour the prey and drink the blood of the slain.”
Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
25 And Balak said to Balaam, “Neither curse him, nor bless him.”
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
26 And he said, “Have I not told you that whatever God would command of me, I would do?”
Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
27 And Balak said to him: “Come and I will lead you to another place. If perhaps it may please God, then you may curse them from there.”
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
28 And when he had led him on to the top of mount Peor, which looks out toward the wilderness,
Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
29 Balaam said to him, “Build seven altars here for me, and prepare as many calves, and the same number of rams.”
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
30 Balak did as Balaam had said, and he placed on each altar a calf and a ram.
Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

< Numbers 23 >