< Numbers 22 >

1 And they set out and made camp in the plains of Moab, across the Jordan, where Jericho is situated.
Sai Isra’ilawa suka kama hanya, suka tafi filayen Mowab, a wajen Urdun, a ƙetare Yeriko, suka yi sansani a can.
2 Then Balak, the son of Zippor, seeing all that Israel had done to the Amorite,
To, fa, Balak ɗan Ziffor ya ga duk abin da Isra’ila suka yi da Amoriyawa.
3 and that the Moabites had great fear of him, and that they were not able to bear his assault,
Sai Mowab ya firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra’ilawa ya kama su.
4 said to those greater by birth of Midian: “So will this people wipe away all those who are dwelling within our borders, in the same way that the ox is accustomed to tear out grass, all the way to the roots.” At that time, he was king of Moab.
Sai Mowabawa suka ce wa dattawan Midiyawa, “Wannan taron zai lashe duk abin da ya kewaye mu kamar yadda saniya takan lashe ciyawa a fili.” Saboda haka Balak ɗan Ziffor, wanda yake sarkin Mowab a lokacin,
5 Therefore, he sent messengers to Balaam, the son of Beor, a seer who lived above the river of the land of the sons of Ammon, to call him, and to say: “Behold, a people has gone forth from Egypt, which has covered the face of the earth. They are encamped opposite me.
ya aika manzanni su zo da Bala’am ɗan Beyor, wanda yake a Fetor, kusa da Kogi, a ƙasar haihuwarsa. Balak ya ce, “Ga mutane sun fito daga Masar; sun mamaye ƙasar, suka kuma yi sansani kusa da ni.
6 Therefore, come and curse this people, for they are stronger than I am. If only, in some way, I might be able to strike them and to drive them from my land. For I know that he whom you bless shall be blessed, and he whom you curse shall be cursed.”
Ka zo yanzu ka la’anta waɗannan mutane, domin sun fi ƙarfina. Wataƙila zan iya cin nasara a kansu, in kuma kore su daga ƙasar. Gama na sani duk waɗanda ka sa musu albarka, sun zama masu albarka ke nan, waɗanda kuma ka la’anta, sun la’antu ke nan.”
7 And the elders of Moab, and those greater by birth of Midian, continued on, holding the price of divination in their hands. And when they had come to Balaam, and had explained to him all the words of Balak,
Sai dattawan Mowab da na Midiyawa suka tashi, suka ɗauki kuɗi don duba. Da suka zo wurin Bala’am sai suka faɗa masa abin da Balak ya ce.
8 he responded, “Remain for this night, and I will answer with whatever the Lord will say to me.” And while they stayed with Balaam, God came and said to him,
Bala’am ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan faɗa muku abin da Ubangiji ya faɗa mini.” Saboda haka dattawan sarkin Mowab suka zauna da shi.
9 “What do these men want with you?”
Sai Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Su wane ne waɗannan tare da kai?”
10 He responded, “Balak, the son of Zippor, the king of the Moabites has sent to me,
Bala’am ya ce wa Allah, “Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne, ya aiko mini wannan saƙo cewa,
11 saying: ‘Behold, a people, which has gone forth from Egypt, has covered the face of the earth. Come and curse them, so that, in some way, I may be able to fight them and drive them away.’”
‘Ga mutane sun fito daga Masar sun mamaye ƙasar. Ka zo yanzu ka la’anta mini su. Wataƙila ta haka zan yi nasara a kansu, in kuma kore su.’”
12 And God said to Balaam, “Do not go with them, and do not curse the people, for they are blessed.”
Amma Allah ya ce wa Bala’am, “Kada ka tafi tare da su. Kada ka la’anta mutanen nan, gama su masu albarka ne.”
13 And he, rising up in the morning, said to the leaders, “Go into your own land, for the Lord has prohibited me from going with you.”
Kashegari Bala’am ya tashi ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, domin Ubangiji ya hana ni in tafi tare da ku.”
14 Returning, the leaders said to Balak, “Balaam was not willing to come with us.”
Saboda haka dattawan Mowab suka koma wurin Balak suka ce, “Bala’am ya ƙi yă zo tare da mu.”
15 Again, he sent many more persons, and these were more noble than those he had sent before.
Sai Balak ya aika waɗansu dattawa masu yawa, masu daraja kuma fiye da na dā.
16 And when these had come to Balaam, they said: “So says Balak, the son of Zippor. Do not hesitate to come to me.
Suka zo wurin Bala’am suka ce, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, Kada ka bar wani abu yă hana ka zuwa wurina,
17 For I am ready to honor you, and whatever you would want, I shall give to you. Come and curse this people.”
gama zan ba ka lada mai yawa in kuma yi duk abin da ka ce. Ka zo ka la’anta mini waɗannan mutane.”
18 Balaam responded: “Even if Balak were to give to me his own house, filled with silver and gold, I still would not be able to change the word of the Lord my God, neither to say more, nor to say less.
Amma Bala’am ya amsa musu ya ce, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba.
19 I beg you to remain for this night also, so that I may know what the Lord will answer me again.”
To, fa, sai ku kwana a nan kamar yadda waɗancan suka yi, ni kuma in roƙi Ubangiji, in ji, wace magana zai ce mini.”
20 Therefore, God came to Balaam in the night, and said to him: “If these men have arrived to call you, then rise up and go with them; yet only in so far as you shall do what I will command you.”
A wannan dare, Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Da yake waɗannan mutane sun zo su tafi da kai, to, ka tafi tare da su, sai dai ka yi abin da na ce ka yi ne kaɗai.”
21 Balaam rose up in the morning, and saddling his donkey, he set out with them.
Bala’am ya tashi da safe, ya ɗaura wa jakarsa sirdi, ya tafi tare da dattawan Mowab.
22 And God was angry. And an Angel of the Lord stood in the way opposite Balaam, who was sitting on the donkey, and he had two servants with him.
Amma Allah ya husata sa’ad da ya tafi, mala’ikan Ubangiji kuwa ya tsaya a hanya don yă hana shi. Bala’am kuwa yana kan jakarsa tare da bayinsa biyu.
23 The donkey, discerning that the Angel was standing in the way with a drawn sword, turned herself from the road and went through a field. And when Balaam beat her and intended to return her to the path,
Da jakar ta hangi mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga jeji. Bala’am kuwa ya buge ta don tă koma hanya.
24 the Angel stood in a narrow place between the two walls, with which the vineyards were enclosed.
Sai mala’ikan Ubangiji ya tsaya a wata matsattsiyar hanya tsakanin gonaki inabi biyu, da bango a kowane gefe.
25 And the donkey, seeing this, drew herself close to the wall and scraped the foot of the rider. So he beat her again.
Sa’ad da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta matse a jikin bango, ta goge ƙafar Bala’am da bangon. Saboda haka sai Bala’am ya sāke bugunta.
26 And, nevertheless, the Angel passing on to a narrow place, where one would not be able to deviate either to the right or to the left, stood to meet him.
Sai mala’ikan Ubangiji ya sha gabansa, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa dama ko hagu.
27 And when the donkey had seen the Angel standing there, she fell under the feet of the rider, who, being angry, struck her sides more vehemently with a club.
Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙasa, Bala’am kuwa ya husata, sai ya buge ta da sandansa.
28 And the Lord opened the mouth of the donkey, and she said: “What have I done to you? Why do strike you me, behold now, for the third time?”
Ubangiji ya buɗe bakin jakar, sai jakar ta ce wa Bala’am, “Me na yi maka da ka buge ni har sau uku?”
29 Balaam responded, “Because you have deserved it, and you have mistreated me. If only I had a sword, so that I might pierce you.”
Bala’am ya ce wa jakar “Domin kin wulaƙanta ni! Da a ce ina da takobi a hannuna da zan kashe ki nan take.”
30 The donkey said: “Am not I your animal, on which you have always been accustomed to sit, even until this present day? Tell me, when did I ever do the same thing to you.” But he said, “Never.”
Jakar ta ce wa Bala’am, “Ni ba jakarka ba ce wadda kake hawa kullum, har yă zuwa yau? Na taɓa yin maka haka?” Bala’am ya ce, “A’a.”
31 Immediately, the Lord opened the eyes of Balaam, and he saw the Angel standing in the way with a drawn sword, and he reverenced him prone on the ground.
Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanun Bala’am, ya kuwa ga mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a zāre. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki.
32 And the Angel said to him: “Why did you beat your donkey three times? I have come to be an adversary to you, because your way is perverse and contrary to me.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya tambaye shi, “Don me ka buge jakarka har sau uku? Na fito ne don in hana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana.
33 And unless the donkey had turned aside from the way, allowing a place for my opposition, I would have killed you, and she would have lived.”
Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da a ce ba tă kauce ba, lalle da na kashe ka, in kuwa bar ta da rai.”
34 Balaam said: “I have sinned, not knowing that you stood against me. And now, if it displeases you for me to continue on, I will return.”
Bala’am ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Na yi zunubi. Ban san ka tsaya a hanya don ka hana ni ba. Yanzu in ba ka ji daɗin tafiyata, sai in koma.”
35 The Angel said, “Go with them, but be careful not to speak anything other than what I shall instruct you.” And so, he went with the leaders.
Mala’ikan Ubangiji ya ce wa Bala’am, “Ka tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka ne kaɗai za ka faɗa.” Saboda haka Bala’am ya tafi tare da dattawan Balak.
36 And when Balak had heard it, he went out to meet him in a town of the Moabites, which is situated at the furthest borders of Arnon.
Da Balak ya ji cewa Bala’am yana zuwa, sai ya fito, ya tarye shi a garin Mowabawa da suke a iyakar Arnon, a ƙarshen yankinsa.
37 And he said to Balaam: “I sent messengers to call you. Why did you not come to me immediately? Was it because I am not able to pay the cost for your arrival?”
Balak ya ce wa Bala’am, “Ban aika maka saƙo cikin gagawa ba? Me ya sa ba ka zo ba? Ko ban isa in sāka maka ba ne?”
38 He answered him: “Behold, here I am. Am I able to speak anything other than what God will put into my mouth?”
Bala’am ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Dole in faɗa abin da Allah ya ce in faɗa ne kawai.”
39 Therefore, they continued on together, and they arrived at a city, which was at the furthest borders of his kingdom.
Sa’an nan Bala’am ya tafi tare da Balak zuwa Kiriyat-Huzot,
40 And after Balak had killed oxen and sheep, he sent the gifts to Balaam, and to the leaders who were with him.
a can ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bala’am da dattawan da suke tare da shi.
41 Then, when morning arrived, he led him to the heights of Baal, and he gazed upon the most distant portions of the population.
Kashegari, Balak ya ɗauki Bala’am ya kai shi kan Bamot Ba’al, daga can ya iya ganin sassan sansanin Isra’ilawa.

< Numbers 22 >