< Leviticus 9 >

1 Then, the eighth day having arrived, Moses called Aaron and his sons, and those greater by birth from Israel, and he said to Aaron:
A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
2 “Take a calf for sin from the herd, and a ram as a holocaust, both immaculate, and offer them in the sight of the Lord.
Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
3 And to the sons of Israel, you shall say: ‘Take a he-goat for sin, and a calf as well as a lamb, both one-year-old and without blemish, as a holocaust.
Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
4 Take also an ox and a ram for peace offerings. And immolate them before the Lord, offering with the sacrifice of each one fine wheat flour sprinkled with oil. For today the Lord will appear to you.’”
da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
5 And so they brought everything that Moses had ordered before the door of the tabernacle, where, when all the multitude stood together,
Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
6 Moses said: “This is the word, which the Lord has instructed. Accomplish it, and his glory will appear to you.”
Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
7 And he said to Aaron: “Approach toward the altar, and immolate on behalf of your sin. Offer the holocaust, and pray for yourself and for the people. And when you have slain the victim for the people, pray for them, just as the Lord has instructed.”
Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
8 And immediately Aaron, approaching toward the altar, immolated the calf for his sin.
Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
9 And his sons brought its blood to him, and dipping his finger in it, he touched the horns of the altar, and he poured out the remainder at its base.
’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
10 And the fat, and the little kidneys, and the mesh of the liver, which are for sin, he burned upon the altar, just as the Lord had instructed Moses.
A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
11 Yet truly, the flesh and its skins he burned with fire beyond the camp.
Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
12 He also immolated the victim of holocaust. And his sons brought its blood to him, which he poured out all around the altar.
Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
13 And when the victim itself was cut into pieces, they brought him the head and each of the limbs, all of which he burned with fire upon the altar,
Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
14 having first washed the intestines and the feet with water.
Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
15 And making an offering for the sin of the people, he slew the he-goat. And expiating the altar,
Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
16 he accomplished the holocaust,
Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
17 adding to it the sacrifice of the libations, which are to be offered together, and burning them upon the altar, separately from the ceremonies of the morning holocaust.
Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
18 He also immolated the ox, as well as the ram, as peace offerings for the people. And his sons brought him the blood, which he poured out upon the altar all around.
Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
19 Then the fat of the ox, and the rump of the ram, and the two little kidneys with their fat, and the mesh of the liver,
Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
20 they placed upon the breasts. And when the fat had been burned upon the altar,
suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
21 Aaron separated their breasts and the right shoulders, lifting them up in the sight of the Lord, as Moses had instructed.
Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
22 And extending his hands to the people, he blessed them. And so, the victims for sin, and the holocausts, and the peace offerings being completed, he descended.
Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
23 Then Moses and Aaron entered the tabernacle of the testimony, and afterwards came out and blessed the people. And the glory of the Lord appeared to the entire multitude.
Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
24 And, behold, a fire from the Lord devoured the holocaust, and the fat which was on the altar. When the crowd had seen this, they praised the Lord, falling on their faces.
Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.

< Leviticus 9 >