< Leviticus 16 >

1 And the Lord spoke to Moses, after the death of the two sons of Aaron, when they were destroyed for offering strange fire.
Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
2 And he instructed him, saying: Speak to your brother Aaron, so that he may not, at any time, enter into the Sanctuary, which is within the veil, before the propitiatory by which the ark is covered, so that he may not die, (for I will appear in a cloud above the oracle)
Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
3 unless he will have done these things beforehand. He shall offer a calf for sin, and a ram as a holocaust.
“Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
4 He shall be vested with a linen tunic. He shall conceal his nakedness with linen undergarments. He shall be wrapped with a linen belt, and he shall impose a linen headdress on his head. For these are holy vestments. All of these he shall put on, after he has been washed.
Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
5 And he shall receive, from the entire multitude of the sons of Israel, two he-goats for sin, and one ram as a holocaust.
Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
6 And when he has presented the calf, and has prayed for himself and for his own house,
“Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
7 he shall cause the two he-goats to stand in the sight of the Lord at the entrance to the tabernacle of the testimony.
Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
8 And casting lots over them both, one is to be offered to the Lord, and the other is to be the emissary goat.
Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
9 The one whose lot fell out to be offered to the Lord, he shall offer for sin.
Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
10 But the one who is to be the emissary goat shall stand before the Lord, so that he may pour the prayers upon him, and may send him away into the wilderness.
Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
11 After these things have been duly celebrated, he shall offer the calf, and praying for himself and for his own house, he shall immolate it.
“Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
12 And taking up the censer, which he has filled from the burning coals of the altar, and drawing up with his hands the aromatic compound for incense, he shall enter within the veil, into the holy place,
Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
13 so that when the aromatics are placed upon the fire, its cloud and vapor may cover the oracle, which is above the testimony, and he may not die.
Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
14 Likewise, he shall take some of the blood of the calf, and sprinkle it with his finger seven times opposite the propitiatory, toward the east.
Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
15 And when he has slain the he-goat for the sin of the people, he shall carry its blood within the veil, just as he was instructed to do with the blood of the calf, so that he may sprinkle it away from the area of the oracle,
“Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
16 and so that he may expiate the Sanctuary from the uncleanness of the sons of Israel, and from their prevarications and every one of their sins. According to this rite, he shall act toward the tabernacle of the testimony, which is fixed among them in the midst of the filth of their habitation.
Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
17 Let no man be in the tabernacle when the high priest enters the Sanctuary in order to pray for himself, and for his house, and for the entire assembly of Israel, until he exits.
Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
18 And when he has exited to the altar which is before the Lord, let him pray for himself, and taking the blood of the calf, and of the he-goat, let him pour it upon its horns all around.
“Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
19 And sprinkling with his finger seven times, let him expiate and sanctify it from the uncleanness of the sons of Israel.
Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
20 After he has cleansed the Sanctuary, and the tabernacle, and the altar, then let him offer the living goat.
“Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
21 And placing both hands upon its head, let him confess all the iniquities of the sons of Israel, and all of their offenses and sins. And calling these down upon its head, he shall send it away, by means of a man prepared to do so, into the desert.
Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
22 And when the goat has carried all their iniquities into a solitary land, and has been released into the desert,
Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
23 Aaron shall return into the tabernacle of the testimony. And placing aside the vestments, which he had worn before when he entered into the Sanctuary, and leaving them there,
“Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
24 he shall wash his flesh in the holy place, and he shall be clothed in his own garments. And departing afterwards, he shall present his own holocaust and that of the people: he shall pray as much for himself as for the people.
Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
25 And the fat which is offered for sins, he shall burn upon the altar.
Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
26 Yet truly, he who has sent away the emissary goat shall wash his clothes and his body with water, and so he shall enter into the camp.
“Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
27 But the calf and the he-goat, which were immolated for sin, and whose blood was brought into the Sanctuary to complete the expiation, these shall be carried outside the camp and be burned with fire: as with their skins, so also with their flesh and dung.
Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
28 And whoever will have burned them shall wash his clothes and flesh with water, and so he shall enter into the camp.
Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
29 And this shall be to you an everlasting ordinance. In the seventh month, on the tenth day of the month, you shall afflict your souls, and you shall do no work, neither someone native born, nor the newcomer who sojourns among you.
“Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
30 On this day, there shall be atonement for you, and also a cleansing from all your sins. You shall be cleansed in the sight of the Lord.
gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
31 For it is a Sabbath of rest, and you shall afflict your souls as a perpetual observance.
Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
32 And the priest who has been anointed, and whose hands have been consecrated to exercise the priesthood in the place of his father, shall make atonement. And he shall be clothed with the linen robe and the holy vestments.
Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
33 And he shall expiate the Sanctuary and the tabernacle of the testimony and the altar, likewise the priest and all the people.
yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
34 And this shall be to you a perpetual law, that you pray for the sons of Israel, and for all their sins once a year. Therefore, he did just as the Lord had instructed Moses.
“Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Leviticus 16 >